A yau Litinin ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da katin murnar sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin, a matsayin martani ga abokai a jihar Iowa ta kasar Amurka, inda ya ce, Sin da Amurka na da manyan muradun bai daya, da damar yin hadin gwiwa, kuma suna iya zama abokan hulda da aminai.

Ya yi fatan jama’ar kasashen biyu za su kara cudanya da juna, da kara yin mu’amala da juna, da yin aiki tare wajen rubuta labarin abokantaka a tsakanin jama’ar kasashen biyu, da ba da sabbin gudummawa ga ci gaban dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. (Mohammed Yahaya)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Saudiyya za su iya zama abin koyi ga hadin gwiwar yankin, yana mai jaddada cewa hadin kan kasashen musulmi wani lamari ne da ake bukata don samun zaman lafiya, tsaro, da ci gaban tattalin arziki mai dorewa a yankin.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a yayin ganawa da ya yi da ministan tsaron kasar Saudiyya Yarima Khalid bin Salman da tawagarsa a birnin Tehran, bayan da ministan na Saudiyya ya isa babban birnin kasar Iran domin tattauna batutuwan da suka shafi yankin da alakar kasashen biyu.

Shugaban na Iran ya jaddada zurfafa dangantakar addini da al’adu da tarihi a tsakanin kasashen musulmi, yana mai jaddada wajabcin karfafa hadin kai a duniyar musulmi.

Shugabar kasar ta Iran ya ce: al’ummar Saudiyya ‘yan uwanmu ne, kuma tun farkon kama aikin gwamnatinmu, mun yi kokarin karfafa alakar ‘yan uwantaka a tsakanin dukkanin kasashen musulmi. Ya kara da cewa, idan kasashen musulmi suka cimma matsaya ta bai daya da hadin kai na hakika, to gwamnatin yahudawan  sahyoniya ba za ta sake haifar da bala’i irin na kisan  bil’adama a yankin ba kamar yadda suke yi yanzu a zirin Gaza.

Ya kuma tabo batun muhimmancin ajiye bambance-bambance a gefe, da inganta hadin gwiwa a yankin.

Pezeshkian ya jaddada cewa, “Shugabannin kasashen musulmi za su iya yin aiki tare, kuma su gabatar da wani abin koyi na rayuwa tare, da wadata, da ci gaba ga sauran al’ummomi na duniya.

Ya kuma yaba da ra’ayin kafa kungiyoyin aiki na hadin gwiwa a bangarori daban-daban na siyasa, tattalin arziki da tsaro tsakanin Iran da Saudiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya
  • Pezeshkian: Hadin gwiwar Iran da Saudiyya zai zama abin koyi ga dukkanin kasashen yankin
  • Araqchi ya mika rubutaccen sakon Jagora ga Shugaba Putin na Rasha