Aminiya:
2025-03-31@22:18:45 GMT

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari

Published: 27th, January 2025 GMT

Tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya ce ya bayar da hayar ɗaya daga cikin gidaje uku kacal da ya mallaka domin sayen abinci.

Buhari ya faɗi hakan a yayin wani taro na jam’iyyar APC da aka gudanar ranar Litinin a Fadar Gwamnatin Katsina.

Tsohon Shugaban Ƙasar ya ce duk da ya shafe shekaru takwas a kan madafan iko, bai yi amfani da kujerar mulki wajen azurta kansa ba.

“Nijeriya ƙasa ce mai wuyar sha’ani ta fuskar jagoranci amma galibin ’yan ƙasar ba su fahimci hakan ba.

“Ba za a taɓa fahimtar irin sarƙaƙiyar da ke cikin riƙo da akalar jagoranci ba da ma ita kanta Ƙasa Nijeriya sai mutum ya tsinci kansa a kan madafan iko.

“A yanzu na ƙara kyan gani da lafiya fiye da yadda nake a lokacin ina Fadar Gwamnatin Nijeriya.

“Duk wanda ya ganni a yanzu zai ce na samu lafiya fiye da yadda nake a lokacin ina shugabancin Nijeriya.

“Duk da cewa na shafe shekaru takwas a matsayin Shugaban Ƙasa, amma gidaje uku kacal na mallaka — ɗaya a Daura, sai guda biyu a Kaduna.

“A yanzu na bayar da hayar ɗaya daga cikin gidajen da ke Kaduna ina samun kuɗin sayen abinci,” a cewar Buhari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna Muhammadu Buhari

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki

Gwamnatin Jihar Kaduna, ta sanar da shirin ɗaukar ma’aikatan lafiya 1,800 aiki don inganta tsarin Kiwon Lafiya a Matakin Farko (PHC) a faɗin jihar.

Wannan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin ma’aikata da kuma inganta ayyukan kiwon lafiya a jihar.

Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara

Kamar yadda Kwamishiniyar Lafiya, Hajiya Umma Ahmad, ta bayyana, wannan mataki zai taimaka wajen rage yawan mace-macen mata masu juna biyu da yara.

“Wannan mataki zai cike giɓin da ake da shi a cibiyoyin lafiya, domin tabbatar da samun ingantaccen kiwon lafiya ga al’ummar Kaduna,” in ji ta.

Gwamnatin jihar ta fara gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 255 tare da samar da kayan aiki na zamani da magunguna.

Wannan zai bayar da damar kula da cututtuka kamar su ciwon suga, hawan jini, da kuma bayar da agajin gaggawa ga mata masu naƙuda.

“Ingantaccen kiwon lafiya ba gata ba ne, haƙƙi ne,” in ji Hajiya Umma, yayin da ta ke jadadda ƙudirin gwamnatin jihar kan kiwon lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
  • YANZU-YANZU: Gwamnan Edo Ya Kai Ziyarar Jaje Kan Kisan Mafarauta A Uromi
  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Shin Mbappe Zai Iya Maye Gurbin Ronaldo A Real Madrid?
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Gobe take Sallah a Nijeriya
  • Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi
  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Gwamnatin Kaduna za ta ɗauki ma’aikatan lafiya 1,800 aiki