Abinda Ya Faru A Lebanon Nasara Ce Akan Isra’ila

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah  Sheikh Na’im Kassim ya gabatar da jawabi na farko bayan cikar kwanaki 60 daga tsagaita wutar yaki da HKI.

A jawabin nasa sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa a lokuta da dama sun yi tunanin mayar da martani akan keta tsagaita wutar yaki, sai dai an bukace su da su dakata, domin bayar damar a dauki wasu matakai na daban.

Sheikh Na’im Kassim ya zargi Amurka da rashin daukar mataki akan HKI ta dakatar da keta yarjejeniyar da take yi, duk da cewa tana cikin masu sa ido akan tsagaita wutar.

Haka nan kuma ya yi ishara da komawar mutanen kudancin Lebanon zuwa garuruwa da gidajenu duk da harbinsu da sojojin mamaya suke yi.

Sheikh Na’im Kassim ya kara da cewa, wanda duk yake da karama yake kuma jin daukaka a tare da shi, babu abinda zai tsorata shi, da hakan shi ne abinda ya faru.

Sheikh Na’ima ya kuma jinjinawa mahukuntan kasar Lebanon akan kin amincewa da bukatar Amurka na bar wa HKI damar kara tsawon wa’adin zamansu a kudancin Lebanon. Haka kuma ya dorawa Amurka da Faransa da MDD alhakin abinda zai biyo baya idan Isra’ilan ba ta janye ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Sheikh Na im Kassim ya

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris

A Gaza fiye da mutane 1,000 ne Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga watan Maris, tun bayan sake dawo da yaki a Zirin.

Hakan ya sanya adadin falasdinawan da Isra’ila ta kashe tun watan Oktoba ya kai 50,350 tare da raunata 114,400 a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.

Hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza sun kashe akalla Falasdinawa 80 a ranar Lahadi.

Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, an kai mutane 53 da lamarin ya rutsa da su zuwa asibitoci a Gaza a ranar Lahadin, wato ranar farko ta bikin Eid al-Fitr.  

Ma’aikatar ta kara da cewa, “har yanzu da yawan wadanda abin ya shafa na makale a karkashin baraguzan gine-gine, saboda masu ceto ba su iya kai musu dauki.

A ranar 18 ga Maris, ne Isra’ila ta sake dawo da kai farmaki Gaza wanda ya saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni da ta fara aiki a watan Janairu.

Ana kuma tuhumar Isra’ila da laifin kisan kiyashi a gaban kotun kasa da kasa saboda yakin da ta yi da yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • An Hori Dagatan Kasar Zazzau Su Sa Ido Akan Bakin Fuskokin A Yankunan Su
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin tsagaita wuta
  • Masar ta miƙa wa Hamas da Isra’ila tayin yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu
  • Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon