Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, Sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan “jajircewar mutanen kudancin kasar Lebanon fuskantar sojojin HKI’ yan mamaya’ wanda ni tahir amin.

///…A Jiya lahadi be wa’adin ficewar HKI daga yankuna da garuruwan da suka mammaye a kudancin kasar Lebanon, amma karfe 4 da safe yana cika mutanen wadannan yankuna suka kwarara zuwa gidajensi, amma ko da suka isa sai suka ga cewa sojojin kasar Lebanon sun sha shinge don hana mutane wucewa zuwa wadannan wurare, don har yanzun akwai sojojin HKI a yankin suna iya kashe su.

Banda haka sojojin HKI sun kara wayoyin wasu daga cikin mutanen wadannan yankuna, suna fada masu cewa kada su kuskura su shiga wadannan yankuna.

Amma sai jerin gwanon mutoci da barbura da mutane masu takawa da kafa kake gani suna kwarara zuwa gidajensu. Gwamnatin kasar Amurka ta bukaci gwamnatin Lebanon su amince a kara lokacin janyewar sojojin HKI daga wadannan yankuna na kudancin kasar Lebanon, har zuwa 18 ga watan Fabrayru mai zuwa, amma gwamnatin ta ki amincea da hakan.

A jiya Lahadi sojojin HKI sun bude wuta kan wasu mutanen kudancin kasar Lebanon wadanda suke son komawa gidajensu, inda suka kashe mutane 18 suka kuma raunata wasu kimani 100 a yankunan daban daban da suke mamaye da su a kasar ta Lebanon.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto yadda al-amura suka tafiya a kudancin kasar Lebanon a safiyar ranar litinin, inda wasu suke cewa, ai mune makama mafi hatsari na hazbullah, kuma muna nan kassammu ne ba zamu bar kasarmu gay an mamaya ba.

Wasu sun bayyana cewa a shirye suke su yi shahada a kan kasarsu da akamamaye, kamar yadda wasu suka yi amma ba zasu taba ja da baya a kan matsayinsu ba.

A cikin wannan halin ne shugaban kasar faransa Emanuel Macron, wanda kumakasarsa na daga cikin kwamitin da aka kafa don kula da aiwatar da yarjeniyar ta tsagaita budewa juna wuta tsakanin kungiyar Hizbullah da kuma HKI na kwanaki 60.

Daga karshe dai HKI da kuma Amurka sun rasa na yi sai suka fara janyewa daga yankun kasar Lebanin da suke mamaye da su, suna ficewa mutane suna komawa cikin gidajensu a yau Litinin.

Manufar HKI na fara yaki da kungiyar Hizbullah da farko shi ne hanata tallafawa ko shi yakin da ake fafatawa da kungiyoyin masu gwagwarmaya da ita a gaza, ba tare da ta shiga cikekken yaki da kungiyar ba, amma ganin yadda dubabban daruruwan yahudawa a arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye sun kasa komawa gidajensu a yankin, kuma sun zama matsala ga gwamnatin HKI, wannan yasa ta shiga yankin. Gadangan da kungiyar Hizbullah musamman bayan sun sami nasarar kashe shugaban kungiyar Sayyed Hassan Nasarallh.

Amma karfin sojoji da makaman da Hizbullah ta nuna ya kara dulmuya HKI a cikin karin musiba, don hizbullah sun yi amfani da makamai masu linzami wadanda suke kaiwa har gaba da birnin Tel’aviv, ko yafa. A nan ne HKI taga cewa ba zata iya tahammulin musibun ba, don haka sai Amurka ta aika jakadan zuwa kasar Lebanon wacce ta sami nasaran gamsar da kungiyar

Don haka tsagaita budewa juna wuta a Lebanon bukatar HKI ce, kuma saboda gazwarsu shiga kasar Lebanon da kuma isar makaman Hizbullah zuwa cikin tsakiya da ma kudancin kasar Lebanon, har a wasu lokacinda HKI ta rasa sojoji masu yawa a wasu hare-haren Hizbullah.

Amma bayan an tsagauita wuta ne, sai wasu sojojin HKI suka shiga wasu kauyuwa a kasar ta Lebanon suna nemna makaman kungiyar da kuma irin ramukan da suka gina a karakashin kasa don adana makamansu.

Sannan yanzun kuma an tilasta masi ficewa daga kudancin kasar ta Lebanon, idan suna sun wannan tsgaita wuta ta dore, idan kuma sun yi taurine kai ta kuwa za’a koma gidan jiya.

Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon wadannan yankuna da kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi

A safiyar yau litinin ce a nan Iran da kuma wasu kasashen duniya da dama suka gudanar da sallar Idi wanda ya kawo karshen watan Ramadan mai al-farma wanda musulmi suka yi azuminsa daga safe zuwa faduwar rana na tsawon kwanaki 29-ko 30.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa a nan Tehran dubban daruruwan mutanen suka fito zuwa babbar masallacin Imam Khumaini dake tsakiyar birnin Tehran inda suka gudanar da sallah mai raka’o’I biyu tare da jagorancin Jagoran juyin juya halin musulunci a kasar Imam Sayyid Aliyul Khamina’e.

Duk da cewa ana samun babbanci tsakanin musulmi kan ranar ajiye azumun amma akalla ba wanda zai yi azami kasa da kwanaki 29.

A cikin watan dai, musulmi sukan yawaita karatun alkur\ani mai girma da kuma kokarin sanin ma’anarsa da kuma zrfafa tunani a cikinsa.

Har’ila yau watan ne na yawaita sadaka na abinci da kuma duk abinda zai taimakawa masu karamin karfi a tattalin arziki.

Musulmi sukan yawaita addu’a da neman gafarar All..a kan zunubban da suka aiakata sannan suna yawaita salloli.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Ba Za A Iya Dakile Ci Gaban Hakkin Dan Adam Na Xizang Da Kowace Irin Karya Ba
  •  Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Yi Wa Musa Dadis  Camara Afuwa
  •  Iran Ta Yi Allawadai Da Sabon Harin HKI A Kasar Lebanon
  • An Fitar Da “Takardar Ci Gaban Sha’anin Hakkin Dan Adam A Xizang A Sabon Zamani”
  • Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
  • Iran: Ta’addancin sojojin Amurka a kan Yemen ‘barazana’ ne ga zaman lafiyar duniya