Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, Sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan “jajircewar mutanen kudancin kasar Lebanon fuskantar sojojin HKI’ yan mamaya’ wanda ni tahir amin.

///…A Jiya lahadi be wa’adin ficewar HKI daga yankuna da garuruwan da suka mammaye a kudancin kasar Lebanon, amma karfe 4 da safe yana cika mutanen wadannan yankuna suka kwarara zuwa gidajensi, amma ko da suka isa sai suka ga cewa sojojin kasar Lebanon sun sha shinge don hana mutane wucewa zuwa wadannan wurare, don har yanzun akwai sojojin HKI a yankin suna iya kashe su.

Banda haka sojojin HKI sun kara wayoyin wasu daga cikin mutanen wadannan yankuna, suna fada masu cewa kada su kuskura su shiga wadannan yankuna.

Amma sai jerin gwanon mutoci da barbura da mutane masu takawa da kafa kake gani suna kwarara zuwa gidajensu. Gwamnatin kasar Amurka ta bukaci gwamnatin Lebanon su amince a kara lokacin janyewar sojojin HKI daga wadannan yankuna na kudancin kasar Lebanon, har zuwa 18 ga watan Fabrayru mai zuwa, amma gwamnatin ta ki amincea da hakan.

A jiya Lahadi sojojin HKI sun bude wuta kan wasu mutanen kudancin kasar Lebanon wadanda suke son komawa gidajensu, inda suka kashe mutane 18 suka kuma raunata wasu kimani 100 a yankunan daban daban da suke mamaye da su a kasar ta Lebanon.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto yadda al-amura suka tafiya a kudancin kasar Lebanon a safiyar ranar litinin, inda wasu suke cewa, ai mune makama mafi hatsari na hazbullah, kuma muna nan kassammu ne ba zamu bar kasarmu gay an mamaya ba.

Wasu sun bayyana cewa a shirye suke su yi shahada a kan kasarsu da akamamaye, kamar yadda wasu suka yi amma ba zasu taba ja da baya a kan matsayinsu ba.

A cikin wannan halin ne shugaban kasar faransa Emanuel Macron, wanda kumakasarsa na daga cikin kwamitin da aka kafa don kula da aiwatar da yarjeniyar ta tsagaita budewa juna wuta tsakanin kungiyar Hizbullah da kuma HKI na kwanaki 60.

Daga karshe dai HKI da kuma Amurka sun rasa na yi sai suka fara janyewa daga yankun kasar Lebanin da suke mamaye da su, suna ficewa mutane suna komawa cikin gidajensu a yau Litinin.

Manufar HKI na fara yaki da kungiyar Hizbullah da farko shi ne hanata tallafawa ko shi yakin da ake fafatawa da kungiyoyin masu gwagwarmaya da ita a gaza, ba tare da ta shiga cikekken yaki da kungiyar ba, amma ganin yadda dubabban daruruwan yahudawa a arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye sun kasa komawa gidajensu a yankin, kuma sun zama matsala ga gwamnatin HKI, wannan yasa ta shiga yankin. Gadangan da kungiyar Hizbullah musamman bayan sun sami nasarar kashe shugaban kungiyar Sayyed Hassan Nasarallh.

Amma karfin sojoji da makaman da Hizbullah ta nuna ya kara dulmuya HKI a cikin karin musiba, don hizbullah sun yi amfani da makamai masu linzami wadanda suke kaiwa har gaba da birnin Tel’aviv, ko yafa. A nan ne HKI taga cewa ba zata iya tahammulin musibun ba, don haka sai Amurka ta aika jakadan zuwa kasar Lebanon wacce ta sami nasaran gamsar da kungiyar

Don haka tsagaita budewa juna wuta a Lebanon bukatar HKI ce, kuma saboda gazwarsu shiga kasar Lebanon da kuma isar makaman Hizbullah zuwa cikin tsakiya da ma kudancin kasar Lebanon, har a wasu lokacinda HKI ta rasa sojoji masu yawa a wasu hare-haren Hizbullah.

Amma bayan an tsagauita wuta ne, sai wasu sojojin HKI suka shiga wasu kauyuwa a kasar ta Lebanon suna nemna makaman kungiyar da kuma irin ramukan da suka gina a karakashin kasa don adana makamansu.

Sannan yanzun kuma an tilasta masi ficewa daga kudancin kasar ta Lebanon, idan suna sun wannan tsgaita wuta ta dore, idan kuma sun yi taurine kai ta kuwa za’a koma gidan jiya.

Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon wadannan yankuna da kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na kawo sauyi da kuma zamanantar da kafafen yada labarai na Najeriya da watsa shirye-shirye ta hanyar hadin gwiwa da inganta fasaha.

 

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris ne ya bayar da wannan tabbacin a taron manema labarai na 2025 da aka gudanar a cibiyar ‘yan jarida ta kasa da ke Abuja ranar Alhamis.

 

Da yake jawabi bayan dawowar sa daga taron kungiyar masu yada labarai na duniya (NAB) a birnin Las Vegas na kasar Amurka, ministan ya ce taron mai taken “Fasahar, The Trend, The Future,” ya samar da wani dandali na yin cudanya da masu ruwa da tsaki a duniya kan sabbin abubuwa da suka tsara makomar watsa shirye-shirye.

 

Ya ce shigarsa wani bangare ne na kokarin da gwamnatin Tinubu ke yi na bunkasa fasahar na bangaren yada labarai na Najeriya.

 

A cewarsa, “wannan zai tabbatar da kudurin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu sauyi mai dorewa a fagen yada labaran Najeriya.”

 

Ministan ya kuma bayyana irin rawar da ya taka a taron ‘yan kasuwan Najeriya da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa, inda ya gana da jami’an UNESCO kan shirin kafa cibiyar koyar da kafafen yada labarai da wayar da kan jama’a a Abuja. Ana sa ran Cibiyar da aka tsara za ta inganta tare da samarda ƙwararrun ‘yan jarida da haɓaka ayyukan watsa labarai masu dacewa.

 

Ya kuma kara jaddada cewa shirin gabatar da jawabai na ministocin da ake yi da kuma tarukan da aka shirya yi a fadin kasar nan na da nufin tabbatar da gaskiya, hada kan jama’a, da kara dankon zumunci tsakanin gwamnati da ‘yan kasa.

 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, wanda ya bayyana muhimman ci gaban da aka samu a fannin samar da wutar lantarki, wanda ya yi daidai da ajandar gwamnati na bunkasa masana’antu a Najeriya da inganta samar da wutar lantarki a fadin kasar.

 

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • News Fox: Sau 6  Yemen Ta Kakkabo Jiragen Amurka Samfurin Mq 9 A Karkashin Gwamnatin Trump
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun