A Banza Man Kare: Barazana Da Takunkumi Sun Daina Tasiri
Published: 28th, January 2025 GMT
Yanzu shekarar ta 2025 muke ciki, kuma matakin da duniya ke daukawa wajen gudanar da al’amura ya bambanta da shekaru goma da suka gabata. Amma abin takaici shi ne, wasu har yanzu sun nace ma tsoffin dabaru, suna ganin barazanar haraji da takunkumi na iya mamaye duniya, na san kun riga kun san inda na dosa.
Mu dauki Rasha a matayin misali, lokacin da ta fuskanci dimbin takunkumi daga kasashen yamma a 2014 da 2022, da yawa sun yi hasashen durkushewar tattalin arzikinta. Maimakon haka, Rasha ta samar wa kanta mafita ta hanyar tsarin hada-hadar kudi na cikin gida wato SPFS, wanda ba ya bukatar tsarin hada-hadar kudi na yammacin duniya, wannan yunkurin ya yi wa tattalin arzikin Rasha garkuwa tare da aza harsashi na zurfafa dangantakar hada-hadar kudi da kawayenta kamar Turkiya, Kazakhstan, har ma da al’ummomi a Gabas ta Tsakiya, tare da yin watsi da tsarin kasashen Yamma. Hakazalika, Amurka ta hana Turkiya damar amfani da fasaha da wasu kayayyakin aiki na Amurka, kama daga jiragen F-35 zuwa jiragen sama marasa matuka. Sakamakon haka shi ne, a halin yanzu Turkiya na kera wasu daga cikin wadannan kayayyakin aiki da albarkatunta har ma ta fara fitar da kayayyaki zuwa wasu kasashen Gabas ta Tsakiya da Afirka. Haka ma kasashen BRICS su ma sun yi ta sake fasalin ka’idojin cinikayyar duniya. Sun koma ga amfani da nasu kudade wajen gudanar da kasuwanci a tsakaninsu, suna rage dogaro da dalar Amurka. Hakazalika, Brazil da Sin na yin cinikayya da kudaden kasashensu, matakin da Indiya da kawayenta na yankin suke koyi da su. Yanzu dai kan mage ya waye, kuma kasashen duniya sun fahimci cewa hadin gwiwar samun moriyar juna tare da dunkulewar duniya waje guda su ne mafita ga kalubalen da duniya ke fuskanta, kuma wannan shi ne makasudin kafa BRICS. (Mohammed Yahaya)
এছাড়াও পড়ুন:
An Fitar Da “Takardar Ci Gaban Sha’anin Hakkin Dan Adam A Xizang A Sabon Zamani”
A yammacin yau Juma’a ne ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai a birnin Lhasa na jihar Xizang wato Tibet, inda aka fitar da “Takardar bayanin ci gaban sha’anin kare hakkin dan Adam a Tibet a sabon zamani”.
Takardar ta yi nuni da cewa, a ko da yaushe, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar suna mai da hankali kan ayyukan da suka shafi Xizang, kuma suna ci gaba da kyautatawa da raya tsarin mulkin Xizang, da daukar matakai masu inganci don raya tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama’a, da kawo alheri ga jama’a, da inganta hadin kai da ci gaban kabilu, da kuma kare hakkin dan Adam na dukkan kabilun jihar Xizang.
Ta kara da cewa, a halin yanzu, jihar Xizang ta samu kwanciyar hankali a bangaren siyasa, da hadin kan kabilu, da bunkasar tattalin arziki da zamantakewar al’umma, lamarin da ya haifar da wani abin al’ajabi na kare hakkin dan Adam a tudun dusar kankara.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp