Leadership News Hausa:
2025-04-22@07:25:51 GMT

Firaministan Sin Ya Tattauna Da Baki Kwararru Dake Kasar

Published: 28th, January 2025 GMT

Firaministan Sin Ya Tattauna Da Baki Kwararru Dake Kasar

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya gudanar da taron tattaunawa da wakilan baki kwararru wadanda ke aiki a kasar da wadanda suka samu lambar yabo ta Abota ta Gwamnatin Sin.

Yayin taron wanda ya gudana jiya Lahadi, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, Li Qiang ya kuma mika gaisuwar sabuwar shekarar gargajiya ta al’ummar Sinawa da fatan alheri ga bakin kwararru, ya kuma godewa goyon baya da kulawar da suka dade suna bayarwa ga kokarin Sin na zamanantar da kanta.

Har ila yau, ya saurari ra’ayoyi da shawarwarinsu kan ayyukan gwamnatin Sin da manufarta ta gyare-gyare da neman ci gaba.

Shugaba Xi Ya Yaba Da Ci Gaban Kasar Sin Duk Da Kalubalen Da Aka Fuskanta A Shekarar Dragon Ana Shirin Kiranye Ga Ɗan Majalisar Da Ya Bar Kwankwasiyya

Kwararrun wadanda suka hada da ’yan kasashen Birtaniya da Poland da Mali da Romania da Jamus da Pakistan, sun gabatar da jawabai kan maudu’i daban daban, kamar na kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da hadin gwiwar cinikayya da tattalin arziki da musayar al’adu da kuma musaya tsakanin jama’a da raya kwararru da ma cudanyar kasa da kasa.

Mataimakin firaminista Ding Xuexiang ma ya halarci taron. (Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi

Shugaban kungiyar Asa’ib Ahl-Al-Hak, kungiya mai yaki da yan ta’adda a kasar Iraki, ya bayyana cewa idan shugaban kasar Siriya mai ci Abu Muhammad Al-Jolani ya kuskura ya taka kasar Iraki ana iya tsare shi sabuda gwamnatin kasar Iraki tana da sammashin kama shit un da dadewa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto shugaban kungiyar Qais Al-khazali yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Asabar, ya kuma kara da cewa jita jitan da yake ji na cewa shugaban kasar ta siriya zai zo iraki a nan gaba, bai taso ba, lokacin zuwansa kasar Iraki bai yi ba saboda zarge-zargen da ake masa tun kafin ya kwace shugabancin kasar ta Siriya, akwai matsalolin doka sosai wadanda za’a fuskanta.

Khazali ya kara da cewa, kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu bai da wata matsala, kuma yana amfanar kasashen biyu, amma zuwansa kasar Iraki a nan kusa yana da  matsala, don tun shekara 2014 Jolani shi ne babban kwamnadan HTS, kuma dakarunsa sun yaki dakarunsa a yaki da suka yi da yan ta’adda a lokacin.

Yace bangaren shari’a na kasar Iraki yana cin gashin kansa ne, bangaren zartarwa ba zai hana bangaren shara’a aikinsa ba.

Kafin haka dai firai ministan kasar Iraki Muhammad Shia al-sudani ya hadu da Jolqni a kasar Qatar a cikin yan kwanakin da suka gabata a gaban sarkin Qatar Tamim bin ahli thani

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Papa Roma Farancis
  • Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • An Gayyaci Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Abbas Aragchi Taron Makamashin Nukliya A Amurka
  • Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi
  • Har Yanzu Ruhin Taron Bandung Yana Tare Da Mu Wajen Kara Karya Lagon Babakere
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar