Aminiya:
2025-04-25@20:59:38 GMT

NAJERIYA A YAU: Dabarun Noma Don Samun Kuɗaɗen Shiga

Published: 28th, January 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Akan ce ‘Noma tushen arziƙi’ kuma mutane da dama za su iya bayar da labarin da ke tabbatar da hakan; domin kuwa ko ba komai idan mutum ya samu abinci ya ci ya ƙoshi babban arziƙi ne.

Wasu ’yan Najeriya kan shuka kayan abinci a unguwanninsu don sama wa kansu abincin da za su ci.


Sai dai masana na ganin da waɗannan mutane za su inganta wannan noma da sun sama wa kansu kuɗaɗen shiga.

NAJERIYA A YAU: Dabarun Bunƙasa Kasuwanci Ta Intanet DAGA LARABA: Me Ya sa Matasa Ba sa Ɗaukar Koyarwa A Matsayin Sana’a?

Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan hanyoyin da ’yan Najeriya za su iya bi don sama wa kansu kuɗaɗen shiga bayan sun noma abin da za su ci.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa talauci a Najeriya zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari a cikin shekaru biyar masu zuwa, ciki har da shekarar zaɓe ta 2027.

Wannan hasashe yana ƙunshe ne a cikin rahoton Bankin wanda aka fitar a lokacin taron bazara na Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da ake yi a birnin Washington, D.C., a ƙasar Amurka.

Rahoton ya jaddada cewa duk da wasu nasarorin da aka samu a harkokin tattalin arziki a kwanakin baya, musamman a ɓangaren da ba na man fetur ba a cikin rubu’i na ƙarshe na shekarar 2024, matsalolin da suka shafi dogaro da albarkatun ƙasa da kuma raunin ƙasa na iya kawo cikas ga ci gaba.

A cewar Bankin Duniya, Najeriya, tare da wasu ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni a yankin kudu da Sahara, za su fuskanci ƙaruwar talauci —saɓanin ƙasashen marasa arzikin albarkatu, waɗanda ake tsammanin za su samu raguwar talauci cikin sauri.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

Rahoton ya bayyana cewa, “Ana hasashen talauci zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari tsakanin 2022 zuwa 2027a ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni—ciki har da manyan masu tattalin arziƙo kamar Najeriya da Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.”

A halin da ake ciki, Sanatan da ke wakiltar Ondo ta Kudu, Jimoh Ibrahim, ya yi kira ga ƙasashen a Afirka, Bankin Duniya, da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da su ba da fifiko ga amfani da bayanai don ci gaban Afirka.

Da yake magana a yayin taron bazara na IMF/Bankin Duniya a Washington, D.C., Amurka, Sanata Jimoh Ibrahim ya jaddada muhimmancin bayanai a ci gaban tattalin arziki da siyasa.

Ya ce, “Idan babu bayanai ba, babu wanda zai iya rage aikata laifuka yadda ya kamata ko kuma gudanar da gwamnatin da ke da nufin cimma nasarar rage talauci.”

Ya ƙara da cewa, “Bayanai kan yawan jama’a da cikakkun bayanai na mutane sun nuna cewa ya kamata ’yan ƙasa su mallaki fasfo na tantancewa domin tattara muhimman bayanai game da su wane ne su da kuma abin da suke yi.”

Sanatan ya yi gargadi ga IMF game da yin hasashe ba tare da ingantattun bayanai ba, yana mai cewa irin waɗannan hanyoyin ba su da inganci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • Sama Da Mutane Miliyan 11 Ne Ke Fama Da Ciwon Suga A Najeriya – Farfesa Zubairu Ilyasu
  • Jigawa Za Noma Rabin Shinkafa Da Ake Amfani Da Ita A Nigeria Nan Da 2030
  • Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya
  • Yayin Da Ake Fuskantar Daminar Bana: Sabbin Hare-hare Na Barazana Ga Shirin Wadata Kasa Da Abinci
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Sabuwar Ƙungiyar ‘Yan Bindiga Ta Addabi Jihohin Kwara Da Neja