Guteress Ya Damu Game Da Matakin Trump Na Dakatar Da Taimakon Kasashen Waje Daga Amurka
Published: 28th, January 2025 GMT
Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guteres ya bayyana damuwarsa game da matakin da Shugaba Donald Trump ya dauka na dakatar da taimakon kasashen waje daga Amurka yayin da sabuwar gwamnatin Amurka ke aiwatar da sabbin manufofinta na ketare, kamar yadda mai magana da yawun Guterres ya bayyana.
“Ya yi kira da a yi la’akari da halin da ake ciki don tabbatar da ci gaba da samar da muhimman ayyukan ci gaba da na jin kai ga al’ummomin da ke da rauni a duniya,” in ji Stephane Dujarric ga manema labarai.
” Ya ce akwai al’umomin da suka dogara da wannan tallafin,” inda ya kara da cewa Amurka na “daya daga cikin manyan masu ba da agaji” a duniya.
Kwanaki kadan bayan rantsar da shi, shugaban Amurka Donald Trump ya rattaba hannu kan wata doka, inda ya umurci dukkan hukumomin gwamnatin tarayya da su sanya dokar ta baci na tsawon kwanaki 90 kan taimakon ci gaban kasashen waje da kuma duba shirye-shiryen da ake da su.
“Manufar Amurka ita ce ba za a sake ba da wani taimakon kasashen waje ba ta hanyar da ba ta dace da manufofin ketare na sabon shugaban Amurka ba,”.
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ce an dakatar da duk wani tallafin kudade na shirye-shiryen ba da agajin kasashen waje ban da na manyan kawayenta a Gabas ta Tsakiya, wato Isra’ila da Masar.
Amma umurnin na ranar Juma’a ya kebance tallafin abinci na gaggawa da kuma abubuwan da ke da alaka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen waje
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
Shuwagabannin Afrika ta Kudu, Malasiya da kuma Colombia sun jaddada matsayinsu nah ana jiragen ruwa dauke da makamai zuwa HKI tsayawa a tashishin jiragen Ruwan kasashen su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ta nakalto shugaban Afirka ta kudu, Cyril Ramaphosa, Firaiministan kasar Malasiya Anwar Ibrahim da Shugaban kasar Colmbia Gustavo Petro suna fadar haka a wani rubutun hadin guiwa da aka buga a mujallar ‘Foreign Policy’ na wannan makon.
Shuwagabannin sun bayyana cewa yakin da HKI ta durawa Falasdinawa a Gaza, ya nuna yadda tsarin dokokin kasa da kasa suna gaza tabbatar da adalci a duniya.
Labarin ya kara da cewa : Ko mu hada kai mu tabbatar da dokokin kasa da kasa, ko kuma dukkan tsaron ya rushe.
Sun HKI ta aikata laifukan yaki a Gaza wadanda suka hada shafi al-umma a doron kasa, inda a cikin shekara guda ta kashe mutane kimani 61,000 tare da taimakon manya-manyan kasashen duniya ko kasashen yamma.
Kasashen Malasiya da Colombia dai suna cikin kasashen da suke goyon bayan karar da Afirka ta kudu da shigar kan HKI a kotun ICC, kuma ya zuwa yanzu kotun ta fidda sammacin kama shuwagabnnin HKI biyu, Wato Firay ministan kasar Benyamin Natanyaho da kuma tsohon ministan yakinsa Aut Galant.
Har’ila yau rubutun shuwagabannin uku ya yi tir da manufan shugaban kasar Amurka ta kwace Gaza ko kuma korar Falasdinawa daga kasarsu.