Abba Ya Naɗa Mace A Matsayin Akanta-Janar A Kano, Ya Yi Sabbin Sauye-sauye
Published: 28th, January 2025 GMT
Haka kuma, an naɗa Muhammad Yahaya Liman a matsayin sabon Daraktan Akanta.
Ya samu ƙwarewa a fannonin rahoton kuɗi da sarrafa kuɗi, ana sa ran zai taimaka wajen ƙara ƙarfin tsarin kuɗi na jihar.
An kuma naɗa Akibu Isa Murtala, wanda a baya ya kasance Mataimaki na Musamman a Ofishin Shugaban Ma’aikata, a matsayin Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Gudanarwa.
Aikin sa shi ne kula da gudanar da ayyukan ma’aikatu.
Injiniya Abubakar Sadiq kuma an naɗa a matsayin Mataimakin Manajan Darakta na Hukumar Samar da Ruwa da Tsabtace Muhalli a Ƙauyuka (RUWASA).
An ɗora masa alhakin inganta samar da ruwa da tsabtace muhalli a yankunan karkara.
Haka kuma, an kafa kwamiti na musamman domin farfaɗo da Hukumar Sufuri ta Jihar Kano (Kano Line).
Sa’idu Abdullahi Shu’aibu zai jagoranci kwamitin a matsayin Shugaba kuma Muƙaddashin Manajan Darakta, inda za su duba tare da tsara ayyukan Kano Line cikin watanni shida masu zuwa.
Gwamna Abba ya yi kira ga dukkanin sabbin jami’an da aka naɗa da su jajirce tare da nuna ƙwarewa, amana, da gaskiya wajen gudanar da ayyukansu.
Ya sake jaddada muhimmancin rawar da za su taka wajen ci gaban Jihar Kano.
কীওয়ার্ড: Gwamnatin
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Amurka na da hannu a ayyukan haramtacciyar kasar Isra’ila na yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.
A wata ganawa da ya yi da Hans Grundberg, wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Yemen a birnin Tehran, Araghchi ya yi Allah wadai da ci gaba da hare-haren soji da Amurka ke kaiwa sassa daban-daban na kasar Yeman, wanda ke sanadin mutuwar fararen hula da kuma lalata kayayyakin more rayuwa.
Ya kara da cewa: Hare-haren da sojojin Amurka suke kai wa kasar Yamen, wanda ya zo daidai da irin yadda gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da aiwatar da kisan gilla a zirin Gaza da kuma hare-haren da take kaiwa kasashen Lebanon da Siriya, wata alama ce kawai da ke nuna irin hadin kai da Amurka take yi da Isra’ia wajen rashin bin doka da oda da kuma yadda take da alaka da ayyukan Isra’ila wajen yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.
Ya bayyana cewa Amurka tana da rashin fahimtar mutanen Yemen, wanda kuma yana da kyau ‘yan siyasar Amurka da su gane cewa ci gaba da mamaye da kisan kiyashi a Falasdinu shine tushen rashin tsaro a yankin.
Dole ‘yan siyasar Amurka su fahimci cewa Amurka ba za su iya da’awar maido da kwanciyar hankali a yankin ba ta hanyar kai hari kan Yemen da kashe mutanen Yemen da ba su ji ba ba su gani ba,” in ji Araghchi.
Ya kara da cewa laifin al’ummar kasar Yaman shi ne hadin kai da goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da ake zalunta.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kin daukar wani mataki dangane da keta ka’idojin yarjejeniyar MDD da kuma dokokin kasa da kasa da gwamnatocin Amurka da Isra’ila suke yi.
Ya ce ya kamata Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakai cikin gaggawa don kawo karshen karya doka da rashin mutunta ka’idojin kasa da kasa.