Qassem : Al’ummar Labanon Ba Za Su Manta Da Irin Goyon Bayan Da Iran Da Iraki Ta Yi Musu Ba
Published: 28th, January 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ce al’ummar kasar Labanon ba za su manta da irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Iraki ta yi musu ba a lokacin da Isra’ila ke kai musu hare-hare.
Sheikh Naim Qassem ya bayyana hakan ne a wani jawabi da aka watsa kai tsaye a yammacin jiya Litinin.
“Nasarar Gaza ta al’ummar Falasdinu ce, da al’ummomin yankin da suka tallafa musu da kuma duk masu neman ‘yanci a fadin duniya.” Inji shi.
Sheikh Qassem ya jaddada cewa tsayin daka wani zabi ne na siyasa, kasa da kuma jin kai don fuskantar mamayar Isra’ila da ‘yantar da yankunan da ta mamaye.
Ya bayyana cewa an cimma manufofin da ke tattare da farmakin Operation Al-Aqsa wanda kungiyoyin gwagwarmaya na Gaza suka kaddamar a ranar 7 ga Oktoba, 2023.
Sheikh Qassem ya bayyana hare-haren da Isra’ila ke kai wa kan Lebanon da zirin Gaza a matsayin wani harin wuce gona da iri da Amurka da wasu gwamnatocin kasashen yammacin duniya ke goyon bayansu.
Ya ce, kungiyar Hizbullah ta tabbatar da cewa tana da hadin kai ta kuma cike gibin shugabanci cikin kankanin lokaci bayan kisan babban sakatarenta Sayyed Hassan Nasrallah a wani kazamin harin da Isra’ila ta kai a kudancin Beirut a karshen watan Satumba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa” a yayin farmakin da ya kashe ma’aikatan jinya 15 a cikin watan Maris a zirin Gaza, wanda ya saba wa sakamakon wani rahoton bincike na cikin gida da sojojin Isra’ila suka fitar.
Wani jami’in tsaron farar hula a Gaza Mohammed al-Moughair ya shaidawa AFP cewa “Bidiyon da daya daga cikin ma’aikatan jinya ya dauka ya tabbatar da cewa rahoton da sojojin Isra’ila suka fitar akwai karairayi a ciki saboda ta aiwatar da hukuncin kisa.
Al-Moughair ya kuma zargi Isra’ila da neman kaucewa abinda ya wajaba kanta a karkashin dokokin kasa da kasa.
Tunda farko dama Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi watsi da rahoton da sojin Isra’ila suka fitar kan kisan da aka yi wa sama da jami’an agajin gaggawa na Gaza a watan da ya gabata, wanda gwamnatin kasar ta ce an kashe ne ta bisa kuskure.
Kungiyar ta yi fatali da rahoton na Isra’ila da cewa ba shi da inganci kuma ba za a amince da shi ba, tana mai jaddada cewa yana cike da karairayi.
A wani rahoto da suka fitar ka abinda ya faru sojojin Isra’ila sun yi ikirarin cewa, an samu ” kura-kurai da yawa” a kisan da akayi wa jami’an agajin a Gaza, suna masu cewa za a kori wani kwamandan sojoji.
“Binciken ya nuna cewa an samu wasu matsaloli na rashin da’a na kwararru, da rashin bin umarni, da kuma gaza yin cikakken bayani kan lamarin,” in ji rundunar.
A ranar 23 ga Maris, ne aka harbe wasu ma’aikatan agaji na Falasdinawa 15 da masu aikin ceto a kusa da Rafah da ke kudancin Gaza.
Kisan da akayi wa jami’an agajin gaggawa na falasdinu ya fuskanci tofin Allah-tsine daga kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama.