Kwamitin Zaman Lafiya Da Tsaro Na AU Yai Yi Zaman Gaggawa Kan Halin Da Ake Ciki A Gabashin DRC
Published: 28th, January 2025 GMT
Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka ya sanar da cewa zai gudanar da zaman gaggawa yau Talata kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango (DRC).
Kwamitin na (PSC) zai gudanar da wani zaman gaggawa a yau Talata kan halin da ake ciki a yankin, wanda ke fama da yakin da ake yi tsakanin dakarun Kongo da mayakan M23″ in ji Paschal Chem-Langhee, mai magana da yawun kwamitin, yayin da al’amura ke kazanta a Goma, babban birnin gabashin DRC.
Kafin nan daruruwan ma’aikatan MDD da fararen hula a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kongo sun tsere zuwa makociyar kasar, Rwanda, yayin da gomman sojojin Kongo din suka “mika wuya” ga jami’an tsaron Rwanda a ranar Litinin, bayan ‘yan tawayen M23 sun kwace iko da birnin na Goma mai muhimmanci a Kongo.
‘Yan tawayen na M23, waɗanda ake zargin suna samun goyon bayan Rwanda, sun zafafa hare-hare a gabashin Kongo a makon jiya, inda suka kwace muhimman birane, Sai dai Shugaban Rwanda Paul Kagame ya sha musanta zargin cewa yana goyon bayan ‘yan tawayen.
Shugaban Kenya William Ruto, wanda yake shugabancin kasashen Gabashin Afirka ya sanar a ranar Lahadi cewa, kungiyar za ta gudanar da wani taro na musamman a cikin sa’o’i 48 don tunkarar rikicin da yake yaduwa a Jamhuriyar Dimukuradiyar Kongo.
Ruto ya tabbatar da cewa tun da farko ya tattauna da Shugaban DRC Kongo Felix Tshisekedi da Shugaban Rwanda Paul Kagame, wadanda dukkansu suka amince za su halarci taron.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House
Cecekucen dai a tsakanin Donald Trump da kuma Vladmir Zylinesky an yi shi ne saboda banbancin ra’ayin da bangarorin biyu suke da shi akan batun kawo karshen yakin Ukiraniya.
Shugaban Amurka Donald Trump dai yana son ganon takwaransa na Ukiraniyan ya amince da kawo karshen yankin da kasarsa take yi da Rasha, yayin da Zylinesky yake Magana akan wasu sharudda kafin hakan ta faru.
Shugaban kasar Amurkan ya yi wa shugaban kasar Ukiraniya goron cewa, kasarsa ce take ba su taimakon kudade da makamai, yana mai kara da cewa; Ko dai ya amince da kulla yarjejeniyar kawo karshen yakin ko kuma Amurka ta dakatar da duk wani taimako.
Haka nan kuma shugaban na Amurka ya zargi shugaban Ukiraniya da cewa, yana son kunna wutar yakin duniya na uku,alhali bai taki komai ba.
Shi kuwa mataimakin shugaban kasar Amurka ya zargi Zylenisky da cewa , babu girmamawa ga Amurka da shugaban kasarta a cikin abinda yake yi..”
Shi kuwa shugaban kasar ta Ukiraniya ya ce, babu yadda za ayi , ya yi sasauci a gaban Putin na Rasha.”
Shugaban na Ukiraniya ya fice daga fadar White House ba tare da gabatar da taron manema labaru ba, kamar yadda tun da fari a ka tsara za a yi.
Bayan tafiyar tashi ne dai shugaban Amurka ya wallafa sako a shafinsa na “Truth Social” da a ciki ya bayyana cewa: Zylinesky ya wulakanta Amurka, amma zai iya dawowa idan ya shirya karbar zaman lafiya.”