Falasdinawa 300,000 Sun Koma Gaza Bayan Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila
Published: 28th, January 2025 GMT
Ofishin yada labarai na gwamnati a zirin Gaza ya sanar da cewa Falasdinawa kusan 300,000 da suka rasa matsugunansu ne suka koma gida a gabar tekun a ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma da kungiyar Hamas.
“Wannan ya zo ne bayan kwanaki 470 na kisan kiyashi da sojojin mamaya na Isra’ila suka yi,” in ji sanarwar, wanda ya yi sanadin shahadar Falasdinawa akalla 47,000 tare da lalata wargaza yankin Falasdinawan.
An bayyana cewa sama da kashi 90%, yankin ya lalace sakamakon hare haren Isra’ila.
An ruguza duk wasu wurare da cibiyoyi masu matukar mahimmanci kama daga asibitoci, makarantu, gidajen jama’a wuraren samar da ruwan sha da wutar lantarki.
A yanzu Falasdinawan dake komawa wannan yankin na da bukatar tallafin gaggawa musamman tantuna da wurin kwanci da ruwa mai tsafta da abinci da kula ta kiwon lafiya da dai sauransu inji kungiyoyin agaji.
“Muna kira ga al’ummomin kasa da kasa, kungiyoyin kasa da kasa da na Majalisar Dinkin Duniya, da kuma kasashen Larabawa dasu samar da wadanan kayayakin ga al’ummar falasdinu inji kungiyoyin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
A Kalla Falasdinawa 35 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; A kalla mutane 35 ne su ka yi shahada, yayin da wasu 62 kuma su ka jikkata a cikin sa’o’i 24.
Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Gaza ta kara da cewa; Sojojin Mamaya sun kai wasu hare-hare a gabashin garin Beit-Hanun dake arewacin Gaza.
A cikin hemar ‘yan hijira dake tsakiyar Gaza, Falasdinawa 3 sun yi shahada, bayan da jiragen saman a ‘yan mamaya su ka kai hari.
A kudancin Gaza kuwa sojojin HKI sun tarwatsa wani gini na fararen hula a yankin Misbah dake arewacin birnin Rafah.
Daga ranar 18 ga watan Maris na wannan shekarar zuwa yanzu adadin Falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 1864, yayin da wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 4890.
Daga 7 ga watan Oktoba 2023 zuwa yanzu jumillar Falasdinawa da su ka yi shahada sun kai 51,240, sai kuma wani adadin da ya kai na mutane 116, 931, da su ka jikkata.
A gefe daya,kafafen watsa labarun HKI sun bayar da labarin cewa, wani yanayi mai tsanani ya faru a Gaza a yau Litinin,da hakan yake nufin cewa an kai wa sojojinsu hari mai tsanani wanda zai iya zama halaka wasu daga cikinsu. Haka nan kuma kafafen watsa labarun na HKI sun ambaci cewa; Uku daga cikin sojojinta sun jikkata saboda fashewar wata nakiya da aka dasa a bakin hanya a Beit-Hanun dake arewacin Gaza.