Aminiya:
2025-04-22@17:46:18 GMT

Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba kwangilar N2.8bn

Published: 28th, January 2025 GMT

Wani shaida ya bayyana wa kotu yadda tsohon Ministan Sufurin Jirgin Sama Sanata Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba aikin gyaran Filin jirgin Katsina a kan Naira biliyan 2.8.

tsohon Daraktan Sayayya ne a ma’aikatar, Musa Obinyan ya bayyana wa kotu cewa a lokacin da Hadi Sirika yake ministan ba wa Kamfanin Al Buraq Investment Ltd, aikin gyaran filin jirgin, alhalin kamfanin bai cancanci a ba shi aikin ba.

Musa Obinyan ya shaida wa Babbar Kotun Abuja cewa rufa-rufa aka yi aka ba wa Al-Buraq, sannan nemo kuɗin aikin aka yi daga wani wuri aka biya.

Ya ba da shaida ne a ci gaba da sauraron shari’ar da Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziƙin (EFCC) take tuhumar Hadi Sirika da badaƙalar Naira biliyan 19.4.

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike

Hukumar EFCC na zargin Hadi Sirika da laifuka 10 da suke da alaƙa da almundahana a lokacin da yake ministan sufurin jiragen sama.

Daga cikin laifukan, ana zargin tsohon, da ba da kwangila ga kamfanin Enginos Nigeria Ltd mallakin ƙaninsa, Abubakar Sirika.

Obinyan ya ƙara da cewa an sanya Alburak da Enginos a matsayin abubuwa daban-daban a kasafin ma’aikatar, amma daga bisani aka gano cewa bayanansu ɗaya a sashen sayen kayayyaki na ma’aikatar.

A baya an gurfanar da Hadi Sirika tare da ’yarsa Fatima Hadi Sirika, da surukinsa, Jalal Sule Hamma tare da kamfanin Al Buraq Global Investment Ltd.

Kotu ta ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga watan Maris, 2025.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Buraq kwangila

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da barazanar HKI na kaiwa cibiyoyin makamashin nukliyar kasar don hana kasar abinda take kira makaman Nukliya.

Ministan ya kara da cewa kasar Iran zata iya kare kanta ko da Amurka ce ta takaleta, kuma Amurka ta san hakan. Sannan ya ce HKI bata taba kaiwa Iran hari a bay aba kuma ba zata taba kai mata hari ba.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya buga wannan labarin a jiya Asabar ya kuma nakalto ministan yana cewa kasashen Rasha da Iran basu taba karfafa dangantakar tsakaninsu fiye da yanzu ba.

Aragchi ya kara da cewa kasashen Iran Rasha da kuma China suna aiki tare don tabbatar da zaman lafiya a duniya a cikin yan shekarun da suka gabata. Kuma kasashen da gaske suke a kan hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hanyoyin da za a magance rikicin Filato — Masana
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • Shugaban Ma’aikatar Shari’a Yana Halartar Taro A Kasar China
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
  • New York Times : Amurka na son rage ofisoshin jakadncinta a Afirka
  • Ango ya tsere tare da surukarsa
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin: Dole Ne Amurka Ta Daina Dora Laifi Kan Sauran Kasashe