Aminiya:
2025-04-02@14:30:48 GMT

Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba kwangilar N2.8bn

Published: 28th, January 2025 GMT

Wani shaida ya bayyana wa kotu yadda tsohon Ministan Sufurin Jirgin Sama Sanata Hadi Sirika ya ba wa kamfanin da bai cancanta ba aikin gyaran Filin jirgin Katsina a kan Naira biliyan 2.8.

tsohon Daraktan Sayayya ne a ma’aikatar, Musa Obinyan ya bayyana wa kotu cewa a lokacin da Hadi Sirika yake ministan ba wa Kamfanin Al Buraq Investment Ltd, aikin gyaran filin jirgin, alhalin kamfanin bai cancanci a ba shi aikin ba.

Musa Obinyan ya shaida wa Babbar Kotun Abuja cewa rufa-rufa aka yi aka ba wa Al-Buraq, sannan nemo kuɗin aikin aka yi daga wani wuri aka biya.

Ya ba da shaida ne a ci gaba da sauraron shari’ar da Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziƙin (EFCC) take tuhumar Hadi Sirika da badaƙalar Naira biliyan 19.4.

Da kuɗin hayar gidana da ke Kaduna nake sayen abinci a yanzu — Buhari ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike

Hukumar EFCC na zargin Hadi Sirika da laifuka 10 da suke da alaƙa da almundahana a lokacin da yake ministan sufurin jiragen sama.

Daga cikin laifukan, ana zargin tsohon, da ba da kwangila ga kamfanin Enginos Nigeria Ltd mallakin ƙaninsa, Abubakar Sirika.

Obinyan ya ƙara da cewa an sanya Alburak da Enginos a matsayin abubuwa daban-daban a kasafin ma’aikatar, amma daga bisani aka gano cewa bayanansu ɗaya a sashen sayen kayayyaki na ma’aikatar.

A baya an gurfanar da Hadi Sirika tare da ’yarsa Fatima Hadi Sirika, da surukinsa, Jalal Sule Hamma tare da kamfanin Al Buraq Global Investment Ltd.

Kotu ta ɗage shari’ar zuwa ranar 10 ga watan Maris, 2025.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Al Buraq kwangila

এছাড়াও পড়ুন:

Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina

Iyayen Abdulsalam Rabi’u Faskari, wanda aka sace tare da mahaifinsa a Jihar Katsina, sun bayyana cewa sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Abdulsalam, wanda ya lashe gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa da aka gudanar a Jihar Kebbi, an sace shi tare da mahaifinsa da wasu makonni biyu da suka gabata, bayan Gwamnan Katsina ya karrama shi.

Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi. Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Mahaifinsa, Malam Rabiu Zakariya Faskari, ya shaida cewa suna tsare a hannun ’yan bindiga a Katsina har sai da wani babban ɗan bindiga mai suna Yellow daga Zamfara ya zo ya karɓe su da ƙarfi.

“Ya yi wa masu garkuwa duka kafin ya tafi da mu,” in ji shi.

Ya ce an yi ciniki kan fansa amma Yellow ya ƙi yarda.

“Muna ta addu’a har ranar Juma’a da aka zo aka ce mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauke mu suka kai mu wani gari, daga nan muka yi tafiyar awa huɗu kafin muka samu mota.”

Malam Rabiu, ya ce da suka hau babur sai direban ya shaida musu cewa an kashe Yellow.

“Ashe mutuwarsa ce ta sa yaransa suka sake mu muka koma gida.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana
  • Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Gwamnan Edo Ya Ziyarci Sanata Barau Kan Kisan Yan Arewa 16
  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Al-Burhan: Sudan Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da RSF Ba
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina