Leadership News Hausa:
2025-04-23@23:07:48 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

Published: 28th, January 2025 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

“Ƙungiyar Al-Hilal ta gode wa Neymar bisa gudunmuwar da ya bayar, kuma tana masa fatan alheri a nan gaba,” in ji ƙungiyar.

Wannan matakin ya zo ne yayin da ya rage wata bakwai kafin ƙarshen kwantaragin Neymar, wanda ya kai shekara biyu da ƙungiyar.

A Al-Hilal, ana biyan Neymar Yuro miliyan 150 a shekara.

Lokacin da ya koma ƙungiyar, Neymar ya bayyana burinsa na kafa tarihi, amma raunin da ya samu yayin wasan Brazil da Uruguay a shekarar 2023 ya hana shi buga wasanni da dama.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Brazil Neymar Raba Gari Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa babu wani kamfen batanci da zai hana Gwamna Dauda Lawal aiwatar da ayyukan da suka shafi al’umma a fadin jihar.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai da sadarwa na gwamna, Malam Salihu Nuhu Anka ya rabawa manema labarai a Gusau.

 

A cewar Anka, Gwamna Lawal ya fara aiki ne a wani aikin ceto, kuma tuni mazauna jihar suka fara cin ribar dimokuradiyya.

 

Ya bayyana cewa hankalinsa ya karkata ne kan kalaman da ya bayyana a matsayin maras tushe da wani tsohon Kwamishinan Yada Labarai, Ibrahim Magaji Dosara ya yi, yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya kalubalanci kalaman da Gwamna Lawal ya yi a wata hira da ya yi da shi kwanan nan.

 

“A yayin taron manema labarai, Dosara ya kai wa Gwamna Dauda Lawal hari cikin rashin kunya a kokarinsa na burge tsohon Gwamna Bello Matawalle,” Anka ya yi zargin.

 

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi
  • Sabuwar Ƙungiyar ‘Yan Bindiga Ta Addabi Jihohin Kwara Da Neja
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe
  • Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.