Leadership News Hausa:
2025-03-02@20:26:25 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

Published: 28th, January 2025 GMT

Al-Hilal Ta Raba Gari Da Neymar

“Ƙungiyar Al-Hilal ta gode wa Neymar bisa gudunmuwar da ya bayar, kuma tana masa fatan alheri a nan gaba,” in ji ƙungiyar.

Wannan matakin ya zo ne yayin da ya rage wata bakwai kafin ƙarshen kwantaragin Neymar, wanda ya kai shekara biyu da ƙungiyar.

A Al-Hilal, ana biyan Neymar Yuro miliyan 150 a shekara.

Lokacin da ya koma ƙungiyar, Neymar ya bayyana burinsa na kafa tarihi, amma raunin da ya samu yayin wasan Brazil da Uruguay a shekarar 2023 ya hana shi buga wasanni da dama.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Brazil Neymar Raba Gari Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250

Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Jihar Kano, ya bai wa jihar da wasu jihohin Arewa kyautar dabino katan 1,250, a matsayin wani ɓangare na shirin tallafin Ramadan na kowace shekara.

Wannan shiri na cikin ayyukan jin-ƙai da Cibiyar Sarki Salman (KSrelief), ke gudanarwa don tallafa wa masu buƙata da kuma ƙarfafa dangantakar Saudiyya da Najeriya.

Ramadan: Ga arahar kayan abinci ga rashin kuɗin saya Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn

Yayin bikin rabon dabinon, Jakadan Saudiyya a Kano, Khalil Admawy, ya gode wa Sarki Salman bin Abdulaziz da Yarima Mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa ƙoƙarinsu na ci gaba da tallafa wa al’ummar Musulmi a faɗin duniya.

Ya jaddada aniyar Saudiyya na ci gaba da taimaka wa Musulmai, musamman a lokacin watan Ramadan.

A bana, Saudiyya ta ware tan 50 na dabino don raba wa a Kano da wasu jihohin Arewa, baya ga tan 60 da aka riga aka aike Abuja a makon da ya gabata.

Ana ci gaba da shirin rabawa don tabbatar da cewa dukkanin kayan sun isa hannun buƙata.

Jakadan Saudiyya, ya kuma bayyana cewa shirin buɗa baki na ƙasar zai fara aiki ne a Abuja a ranar 3 ga watan Ramadan, inda za a raba wa Musulmai masu azumi abinci kyauta.

Ya kuma yi bayani kan irin ayyukan jin-ƙai da Cibiyar Sarkin ke yi a duniya, inda ya ce tuni cibiyar ta kammala sama da ayyuka 2,500 da darajarsu ta haura dala biliyan bakwai, waɗanda suka amfanar da ƙasashe 91.

A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Umar Farouk, ya wakilta, ya nuna godiyarsa ga wannan kyauta.

Ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Kano za ta tabbatar da cewa an raba dabinon ga waɗanda suka dace su amfana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • Saudiyya Ta Raba Tan Hamsin Na Dabino A Nijeriya
  • Shugabar Tanzaniya Ta Yaba Da Yadda Ake Ci Gaba Da Samun Karuwar Jigilar Kayayyaki A Tashar Tanga Da Sin Ta Inganta
  • An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Wasu Kasashen Musulmi Sun Fara Azumin Ramadana A Yau Asabar, Yayin Da Wasu Za Su Fara A Gobe Lahadi
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250
  • Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai