Aminiya:
2025-03-03@09:41:05 GMT

Kotu ta hana ’yan sanda sake taɓa Muhuyi Rimingado 

Published: 28th, January 2025 GMT

Babban Kotun Jihar Kano ta rundunar ’yan sanda sake kamawa, gayyata ko tsare Shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa da Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jihar Jihar Kano (PCACC), Magaji Rimingado.

Kotun ta ba a da umarnin ne bayan  ƙarar da Babban Lauyan jihar Kano da hukumar PCACC da kuma Magaji Magaji Rimingado suka shigar.

Waɗanda ake ƙara su ne rundunar ’yan sandan Najeriya, Sufeto-Janar na ’yan sanda da Mataimakinsa Ma kula da Shiyya ta Ɗaya da Kwamishinan ’Yan Sanda Kano da ASP. Ahmed M. Bello da Bala Muhammad Inuwa.

Kotun ta ɗage shari’ar zuwa ranar 2 ga watan Fabrairu, 2025.

A ranar Juma’a ’yan sanda sun kama shugaba na hukumar da yamma, inda suka tsare shi na tsawon awanni, daga baya ba da belinsa da tsakar dare, tare da umartar sa ya kai kansa hedikwatar rundunar da ke Abuja ranar Litinin don amsa tambayoyi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha

Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan, ya bayyana cewa matarsa ta taɓa kawo masa ƙorafi game da cin zarafin da ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya yi mata.

A cewarsa, rikicin ya fara tun lokacin da Natasha ta tsaya takarar kujerar Sanata a 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar SDP, inda ta nemi kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.

Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano

A lokacin, Akpabio yana riƙe da mukamin Ministan Neja Delta.

“Da kaina na je na same shi na buƙaci ya bai wa matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotar da ke tsakaninmu.

“Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci,” in ji shi.

Bayan zaɓen 2019, Natasha ta sake tsayawa takarar Sanata a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, inda ta samu nasara.

A lokacin, ana raɗe-raɗin cewa Akpabio bai ji daɗin yadda ta samu goyon baya ba, kuma hakan ya ƙara haddasa rashin jituwa a tsakaninsu.

“Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta ci gaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da ta ke fuskanta daga shugaban majalisar.

“Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fi min ita a yanzu domin ita ce farin cikina.”

Natasha dai ta ce tana da wasu hujojji da za ta fitar, wanda ke nuna yadda Akpabio ya neme ta, lamarin da yanzu haka ya haifar da zazzafar muhawara a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɓacewar bindigogi 4,000: Sakaci ne dalili —’Yan sanda
  • Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
  • An kama ɓarayin waya a Kano
  • Gobara Ta Sake Ƙona Kasuwar Kara A Sokoto
  • Ramadan: ’Yan sanda sun tsaurara tsaro saboda azumi a Borno
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano
  • Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai