Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-19@07:45:34 GMT

Tarin Bola Na Haddasa Cutuka Ga Mazauna Tudun Ilu A Kaduna

Published: 28th, January 2025 GMT

Tarin Bola Na Haddasa Cutuka Ga Mazauna Tudun Ilu A Kaduna

Wani katafaren wurin zubar da shara da aka tanada a wajen Kaduna ya koma wata babbar sana’ar kasuwanci inda ‘yan gwangwan ke amfani da gurbataccen ruwan najasa domin amfanin Noma.

 

 

Wata Kungiyar ‘yan jarida ta ziyarci al’ummar Katanga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna inda aka fara gudanar da wannan aiki inda suka gano cewa kimanin ‘yan gwangwan 150 ne suka tsunduma kansu domin karfafa tattalin arziki a wurin da ake jibge sharar.

 

Jama’a na yin tururuwa zuwa wurin zubar da sharar na Katanga wanda shi ne babban wurin da gwamnatin jihar ta amince da sharar don tabbatar da tsaftar muhalli.

 

Mallam Zubairu shi ne shugaba, ya shaidawa tawagar ‘yan jarida da sauran kungiyoyin fararen hula da suka halarci wajen cewa sun fara gano wannan sana’ar ne mai riba fiye da shekaru 3 da suka wuce.

 

Ya ce suna samar da abin da bai gaza Naira 8,000 kullum, kuma suna biyan N1000 a matsayin haraji ga karamar hukumar.

 

Mallam Suleiman Kawosu, wanda ya yi tafiyar sama da Kilomita 70 daga Zariya zuwa wurin.

Ya ce yana sayar da wata motar dakon taki a kan kudi da bai gaza Naira 10,000 don ciyar da iyalansa masu ‘ya’ya 9 da kuma kula da su ba, kuma yana jin dadin wannan sana’ar.

 

A halin da ake ciki kuma tawagar daga baya ta koma Tudun Illu da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa, akwai wani katafaren rumbun da ake zubar da shara ba bisa ka’ida ba da ke da babbar kasuwa a cikin babban birnin jihar.

 

Da yake magana da tawagar, wani basarake a yankin Alhaji Bala Illu ya koka da cewa wurin da ba a amince da shi ba ya wanzu tsawon shekaru da dama kuma kwanan nan ya haddasa gobara a wata makarantar Firamare da ke kusa.

 

Don haka ya bukaci gwamnati ta dauki tsattsauran mataki ta hanyar share wurin tare da dakatar da masu aikata wannan aika-aika daga ayyukan da ba su dace ba.

 

Alhaji Shehu Usman ya tabbatar da abin da basaraken ya fada tun da farko sai dai ya kara da cewa mutane da dama a yankin sun kamu da rashin lafiya sakamakon illar muhalli da sharar ta haifar.

 

Masana yanayi irin su Gloria Kasang Bulus da Zinta Istifanus sun koka kan yadda ake samun juji a tsakiyar wuraren zama a Kaduna.

 

Ziyarar da ‘yan jarida da masu kula da muhalli suka yi ta rangadin wuraren zubar da ruwa na najasa ya kasance irinsa na farko don samun bayanai na farko kan batutuwan da suka shafi muhalli da sauyin yanayi domin su adana bayanansu da kuma bayar da rahoto ga masu iko kan bin kyawawan halaye na muhalli na duniya.

 

Cov/Shindong Bala/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: shara

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74

Hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kaiwa lardin Hudaida ya karu zuwa 74.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar gwamnmatin kasar ta Yemen na fadar haka a yau Jumma’a ta kuma kara da cewa dukkan mutanen da suka mutu a hare-haren jiragen yakin Amurka a cibiyar man fetur na Ras Isa a birnin Hudaida fararen hula ne. babu wani mayakin kungiyar Ansarulla ko guda a cikinsu.

Labarin ya kara da cewa jiragen yakin Amurka wadanda suka taso daga jiragen ruwa masu daukar jiragen sama na Amurka masu suna USS Harru Truman da kuma USS Carl a tekun red sea, sau kai hare kan ras Isa ne har sau biyu, hare na biyun ya fada ne kan ma’aikatan ceto da kuma yan kwana –kwana masu masu kashe wuta da cetun wadanda aka kaiwa hari na farko.

Majiyar Amurka ta bayyana cewa kayakin man fetur da ta kaiwa hari hukumar UNICEF ta MDD ce ta gina don haka kasar Yemen ba zata iya maida suba. Sannan kungiyar Ansarullah na samun kudaden tafiyar da kasar Yemen da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Harin Amurka Na Jiya A Yemen Ya Kai 74
  • Neja Za Ta Kaddamar da Ayyukan Jiragen Sama Daga Filin Jirgin Sama na Bola Ahmed Tinubu.
  • ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna
  • Gazawar Gwamnatin Tinubu Ce Ke Haddasa Zubar Da Jini A Filato – Ƙungiyar Dattawan Arewa
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato
  • UEFA: Wasan Arsenal Da Real Madrid Ya Haddasa Rikici A Tsakanin Magoya Bayan Kungiyoyin A Kano
  • An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna