Tarin Bola Na Haddasa Cutuka Ga Mazauna Tudun Ilu A Kaduna
Published: 28th, January 2025 GMT
Wani katafaren wurin zubar da shara da aka tanada a wajen Kaduna ya koma wata babbar sana’ar kasuwanci inda ‘yan gwangwan ke amfani da gurbataccen ruwan najasa domin amfanin Noma.
Wata Kungiyar ‘yan jarida ta ziyarci al’ummar Katanga da ke karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna inda aka fara gudanar da wannan aiki inda suka gano cewa kimanin ‘yan gwangwan 150 ne suka tsunduma kansu domin karfafa tattalin arziki a wurin da ake jibge sharar.
Jama’a na yin tururuwa zuwa wurin zubar da sharar na Katanga wanda shi ne babban wurin da gwamnatin jihar ta amince da sharar don tabbatar da tsaftar muhalli.
Mallam Zubairu shi ne shugaba, ya shaidawa tawagar ‘yan jarida da sauran kungiyoyin fararen hula da suka halarci wajen cewa sun fara gano wannan sana’ar ne mai riba fiye da shekaru 3 da suka wuce.
Ya ce suna samar da abin da bai gaza Naira 8,000 kullum, kuma suna biyan N1000 a matsayin haraji ga karamar hukumar.
Mallam Suleiman Kawosu, wanda ya yi tafiyar sama da Kilomita 70 daga Zariya zuwa wurin.
Ya ce yana sayar da wata motar dakon taki a kan kudi da bai gaza Naira 10,000 don ciyar da iyalansa masu ‘ya’ya 9 da kuma kula da su ba, kuma yana jin dadin wannan sana’ar.
A halin da ake ciki kuma tawagar daga baya ta koma Tudun Illu da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa, akwai wani katafaren rumbun da ake zubar da shara ba bisa ka’ida ba da ke da babbar kasuwa a cikin babban birnin jihar.
Da yake magana da tawagar, wani basarake a yankin Alhaji Bala Illu ya koka da cewa wurin da ba a amince da shi ba ya wanzu tsawon shekaru da dama kuma kwanan nan ya haddasa gobara a wata makarantar Firamare da ke kusa.
Don haka ya bukaci gwamnati ta dauki tsattsauran mataki ta hanyar share wurin tare da dakatar da masu aikata wannan aika-aika daga ayyukan da ba su dace ba.
Alhaji Shehu Usman ya tabbatar da abin da basaraken ya fada tun da farko sai dai ya kara da cewa mutane da dama a yankin sun kamu da rashin lafiya sakamakon illar muhalli da sharar ta haifar.
Masana yanayi irin su Gloria Kasang Bulus da Zinta Istifanus sun koka kan yadda ake samun juji a tsakiyar wuraren zama a Kaduna.
Ziyarar da ‘yan jarida da masu kula da muhalli suka yi ta rangadin wuraren zubar da ruwa na najasa ya kasance irinsa na farko don samun bayanai na farko kan batutuwan da suka shafi muhalli da sauyin yanayi domin su adana bayanansu da kuma bayar da rahoto ga masu iko kan bin kyawawan halaye na muhalli na duniya.
Cov/Shindong Bala/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: shara
এছাড়াও পড়ুন:
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
Fashin Baƙi:
Wannan magana ta Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa tana bayani ne a kan istigfari ( wato nema gafarar Allah) da sakamakonsa a rayuwar mutum. Domin fahimtar wannan tasa dalla-dalla, zan yi bayani a matakai uku:
Ma’anar Istigfari da Muhimmancinsa:
Istigfari na nufin neman gafarar Allah Ta’ala bisa zunubai da aka aikata. Ana yin hakan ta hanyar faɗin “Astaghfirullah” da sauran lafuzza masu kama da hakan. Allah Maɗaukakin Sarki ya yawaita umurni da a yi istigfari a cikin Alƙur’ani, kamar yadda ya ce:
” sai na ce: Ku nemi gafarar Ubangijinku, lalle Shi Ya kasance Mai ywana gafara ne” Suratu Nuh aya ta 10.
Manzon Allah (S.A.W) yana yawaita istigfari fiye da sau saba’in a rana, kamar yadda hadisi ya tabbatar da haka a cikin Sahihul Bukhari da Muslim..
Sakamakon Istigfari a Bisa Maganar Ibnu Juzai:
Ibnu Juzai yana bayani ne cewa istigfari yana da tasiri a rayuwar mai neman gafara, kuma sakamakonsa yana bayyana a cikin:
Tsayuwa Kan Taƙawa:
Taƙawa tana nufin kiyaye umarnin Allah da guje wa haninsa wato nisantar saɓa masa. Idan mutum yana neman gafarar Allah da gaske, hakan yana ƙarfafa tsoron Allah a zuciyarsa, wanda ke hana shi komawa ga zunubi. Allah Ta’ala Yana cewa:” Kuma ku tuba ga Allah gaba ɗayanku ya ku mummunai domin ku rabauta” Suratun Nur aya ta 31.
Kiyaye Sharuddan Tuba:
Tuba tana da sharuɗa guda uku, idan zunubin ba ya da alaƙa da wani bawa, to sharuɗan guda uku ne, idan kuma yana da alaƙa da wani, to sharuɗan hudu ne kamar haka:
1. Nadama bisa abin da aka aikata.
2. Barin zunubin nan take ba tare da jinkiri ba.
3. Ƙudirin kada a koma ga zunubin nan gaba.
4. Idan ya shafi wani mutum, sai a biya shi haƙƙinsa.
Idan mutum yana istigfari ba tare da kiyaye waɗannan sharuɗa ba, to istigfarinsa ba zai ba yi mass tasiri sosai ba.
Inkarin Saɓo da Zuciya:
Wannan yana nuna cewa zuciyar mai istigfari tana ƙin saɓo kuma tana jin haushin zunuban da aka aikata a baya. Wannan na nufin istigfari na gaskiya yan ƙarfafar bawa a kan aibata saɓo da jin nauyin aika shi. Hakan yana nufin istigfari yana gina halin mutumin da ya fahimci girman zunubi, kuma hakan yana hana shi sake aikata shi.
Muhimmancin Wannan Magana a Rayuwa:
Maganar Ibnu Juzai tana koyar da cewa:
• Istigfari ba kawai furuci ba ne, yana da tasiri ga zuciya da hali.
• Dole ne istigfari ya kasance tare da takawa da gujewa sabo.
• Kiyaye sharuɗan tuba yana tabbatar da cewa istigfarin mutum ya dace da shari’a.
A taƙaice, Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana jaddada cewa istigfari na gaskiya yana haifar da tsayuwa a kan addini, da kiyaye dokokin Allah, da gujewa komawa ga zunubi. Wannan yana nufin cewa nema gafarar Allah ba wai magana ce ta fatar baki kawai ba, sai da aikin zuciya da na gaɓɓai.
Allah ya sa mu kasance cikin masu istigfari na gaskiya!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp