Leadership News Hausa:
2025-04-02@08:04:07 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Published: 28th, January 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Rundunar ƴansandan Abuja, ta bayyana cewa rashin samun labarin lamarin da wuri ne ya kawo jinkirin ɗaukar mataki.

Mun Fara Bincike – Ƴansanda

Kakakin rundunar ƴansandan Abuja, Josephine Adeh, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce tuni suka fara bincike domin ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.

Ta ce: “Ƙarfe 1 na dare muka samu kiran gaggawa cewa ƴan bindiga sun kai hari Chikakore.

Nan take muka tura ƴansanda zuwa yankin. Bincike ya nuna cewa maharan guda bakwai ne, sun yaudari mai gidan har ya buɗe musu ƙofa.”

Ta kuma ce wata maƙwabciyarsu da ta yi ƙoƙarin taimaka musu ta ji rauni, kuma tana karɓar magani a asibiti.

Rundunar ta buƙaci mazauna yankin su kwantar da hankalinsu tare da bayar da haɗin kai wajen bincike.

Fargaba Kan Matsalar Tsaro a Abuja

Wannan harin ya jefa tsoro a zukatan mazauna yankin, musamman waɗanda suka sha fama da matsalolin tsaro a baya.

A farkon watan nan, wasu ƴan bindiga da ake sun tayar da abun fashewa a wata makarantar Islamiyya a ƙauyen Kuchibuyi, Bwari, inda mutane biyu suka rasa rayukansu.

Yankin Bwari, wanda ke maƙwabtaka da jihohin Kaduna da Neja, ya sha fama da hare-haren ƴan bindiga, ciki har da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Wannan ya sa mazauna yankin ke fargabar dawowar zaman ɗar-ɗar a rayuwarsu.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Amurka na da hannu a ayyukan haramtacciyar kasar Isra’ila na yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

A wata ganawa da ya yi da Hans Grundberg, wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Yemen a birnin Tehran, Araghchi ya yi Allah wadai da ci gaba da hare-haren soji da Amurka ke kaiwa sassa daban-daban na kasar Yeman, wanda ke sanadin mutuwar fararen hula da kuma lalata kayayyakin more rayuwa.

Ya kara da cewa: Hare-haren da sojojin Amurka suke kai wa kasar Yamen, wanda ya zo daidai da irin yadda gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da aiwatar da kisan gilla a zirin Gaza da kuma hare-haren da take kaiwa kasashen Lebanon da Siriya, wata alama ce kawai da ke nuna irin hadin kai da Amurka take yi da Isra’ia wajen rashin bin doka da oda da kuma yadda take da alaka da ayyukan Isra’ila wajen yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

Ya bayyana cewa Amurka tana da rashin fahimtar mutanen Yemen, wanda kuma yana da kyau ‘yan siyasar Amurka da su gane cewa ci gaba da mamaye da kisan kiyashi a Falasdinu shine tushen rashin tsaro a yankin.

Dole ‘yan siyasar Amurka su fahimci cewa Amurka ba za su  iya da’awar maido da kwanciyar hankali a yankin ba ta hanyar kai hari kan Yemen da kashe mutanen Yemen da ba su ji ba ba su gani ba,” in ji Araghchi.

Ya kara da cewa laifin al’ummar kasar Yaman shi ne hadin kai da goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kin daukar wani mataki dangane da keta ka’idojin yarjejeniyar MDD da kuma dokokin kasa da kasa da gwamnatocin Amurka da Isra’ila suke yi.

Ya ce ya kamata Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakai cikin gaggawa don kawo karshen karya doka da rashin mutunta ka’idojin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Ramuwar Gayya Kan Takunkumin Biza Da Amurka Ta Kakaba Wa Jami’anta
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Nigeria: Zazzabin “Lassa” Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 118 Tun Farkon Wannan Shekara
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya