An Bukaci Ma’aikatun Gwamnati Su Rika Yin Kasafin Da Zai Amfani ‘Yan Nijeriya
Published: 28th, January 2025 GMT
Kungiyar masu ruwa da tsakin masana’antu a fannin mai ta Najeriya NEITI da hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, na kokarin kwato kusan dala biliyan shida da kuma wani naira biliyan 66 da gwamnatin tarayya ke bin gwamnatin tarayya bashin.
Sakataren zartarwa na hukumar Mista Orji Ogbonnaya Orji, wanda ya bayyana haka a lokacin kare kasafin kudin 2025 a gaban kwamitin majalisar kan albarkatun man fetur.
Mista Orji Ogbonnaya, ya bayyana cewa tuni hukumar ta gabatar da dukkan rahotannin da ta ke a masana’antar hako mai ga majalisar a wani bangare na matakan tabbatar da samun nasarar kwato kudade daga hukumomin gwamnati.
Ya ce wasu daga cikin abubuwan da hukumar ta sa a gaba a shekarar 2025 sun hada da gudanar da rahoton masana’antu na fannin iskar gas da ma’adinai, da tantance kudaden da doka ta tanada, bincike kan ainihin adadin gidaje mai da ake amfani da su a Najeriya, da kuma aiwatar da binciken ra’ayi jama’a na kasa.
Sakataren zartarwa, ya bayyana cewa NEITI a matsayin hukumar da aka kafa domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkar man fetur da iskar gas a Najeriya ciki har da bangaren ma’adinai, ta sami kasafin kudin shekarar 2025 na Naira biliyan 6.5.
A nasa jawabin shugaban kwamitin kula da albarkatun man fetur na majalisar Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ya jaddada muhimmiyar rawar da hukumar ta ke takawa a fannin man fetur, ya kuma ba da tabbacin cewa kwamitin a shirye yake na mara masa baya wajen gudanar da ayyukansa.
Alhaji Alhassan Doguwa, ya shawarci shugabannin hukumar da su ci gaba da sa kaimi ga jin dadin ‘yan Nijeriya a duk lokacin da suke shirya kasafin kudin shekara bisa la’akari da yanayin tattalin arzikin da talakawa ke fuskanta daga sassa daban-daban na kasar nan.
COV: TSIBIRI/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Kasa tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan
Kungiyar Hamas ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su shirya zanga-zangar nuna goyon baya ga Gaza da kuma kin amincewa da kisan kare dangi
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta yi kira ga jami’o’in Yammacin Kogin Jordan da su tashi tsaye wajen gudanar da gangami da zanga-zanga a ranar Talata, domin nuna goyon baya ga Gaza, da tsayin dakanta, da kuma kawo karshen kisan kiyashi.
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, shugaban kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bukaci ‘yan Falasdinu gami da daliban jami’o’in Falasdinu masu ‘yanci a Yammacin Gabar Kogin Jordan da suke mamaye da su da su tashi tsaye tare da gudanar da zanga-zangar bacin rai da aka shirya za a fara a yau Talata, domin nuna goyon baya ga zirin Gaza da kuma yin watsi da yakin da ake yi na kawar da al’ummart yankin.
Jagora Shadid ya jaddada cewa, dole ne kungiyar dalibai a yammacin gabar kogin Jordan ta taka rawa wajen dakatar da kisan kiyashi da kuma daukar matakan gaggawa ga Gaza a dukkanin fagagen jama’a da jami’o’i, yayin da ake ci gaba da yakin kisan kiyashi da kuma fatattakar da ‘yan gwagwarmaya suke ci gaba da gwabza fada a fagen yakin ambaliyar al-Aqsa.