Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-22@03:54:11 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Published: 28th, January 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu gagarumar nasara wajen yaki da miyagun laifuka, inda ta kama wasu da ake zargi da aikata manyan laifuka da dama.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Salman Dogo Garba ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sandan Bompai Kano.

 

Ya ce rundunar ta kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da kuma kashe Alhaji Atiku Mu’azu, mai shekaru 64 da haihuwa mazaunin Janbulo, Kano.

 

Wadanda ake zargin, Abubakar Hassan (wanda aka fi sani da Captain), Adamu Abubakar Adam, da Alhaji Hamisu (wanda aka fi sani da Bakin Bross), an kama su ne bayan wani ci gaba da bincike da jami’an leken asiri suka yi.

 

A wani labarin kuma wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan Alhaji Auwalu da ke Sabuwar Unguwa Garo a karamar hukumar Kabo a Kano, inda suka yi masa fashin Naira miliyan 8 tare da yin garkuwa da ‘yarsa Zainab Aliyu mai shekaru 16.

 

CP Salman Dogo Garba ya ci gaba da cewa, ‘yan sanda sun fara gudanar da bincike domin ceto wanda aka kashe tare da damke wadanda suka aikata laifin.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya ci gaba da bayyana cewa, a wani samame na daban, rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane 17 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da suka abkawa Hotoro a Kawo Kano, inda suka farfasa shaguna da motoci, tare da far wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

 

“An kuma kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da laifin kai hari ga wasu mutane biyu da ba su ji ba ba su gani ba, tare da yi musu fashin wayoyin hannu guda 200 a unguwar Yankatsari da ke Kano.

 

CP Salman Dogo Garba ya bukaci jama’a da su kiyaye da taka tsantsan, kuma su kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su ko kuma ta lambobin hukumar: 08032419754, 08123821575, 09029292926.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda wasu mutane

এছাড়াও পড়ুন:

An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) sun tsallake rijiya da baya da raunukan harbin bindiga bayan da ɓata-gari suka buɗe musu wuta a lokacin da suka kama miyagun ƙwayoyi a Yankin Banban Birnin Tarayya.

Mutum uku daga cikin jami’an sun samu raunuka an harbi, ɗaya a haƙari, biyu a gadon baya da kafafunsu, a yayin harin da aka kai musu a unguwar Jahi, bayan sun kama wasu miyagun ƙwayoyi a ranar Alhamis.

Kakakin NDLEA na ƙasa, Femi Babafemi, ya bayyana cewa an kwantar da jami’an guda uku a asibiti saboda raunukan harbin bindiga da suka samu.

“Lamarin ya faru ne a lokacin da tawagar jami’an NDLEA, bisa bayanan sirri, suka kai samame wani kwangon gini a yankin NNPC da ke unguwar Jahi inda aka ƙwato kwalaben codeine guda 74, codeine ta ruwa lita 10, gram 48 na tramadol mai milligram 225, da kilogiram 4.9 na skunk, wani nau’in tabar wiwi, da kuma wayoyin android guda biyar.

’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo Makarantar Bare: Shekara 20 dalibai na karatu a matsanancin yanayi

“Yayin da tawagar NDLEA ke hanyarsu ta fita daga wurin kuma an kai musu harin bindiga,” in ji Babafemi a cikin sanarwar da ya fitar washegari da daddare.

Babafemi ya ce, an fara ba da kulawar gaggawa ga jami’an da suka ji rauni a asibitin ’yan sanda da ke Garki Area 1 kafin a mayar da su Babban Asibitin Abuja domin ƙarin kulawa.

Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya), ya yaba wa ma’aikatan asibitin ’yan sanda bisa ga agajin gaggawar da suka bayar.

Ya kuma gode wa Shugaban Asibitin Ƙasa, wanda shi da kansa ya tuntube shi domin ya kula da jinyar jami’an da suka ji rauni.

Shugaban NDLEA, wanda ke Kano a kan ayyukan hukuma, ya kuma yi magana ta waya da jami’an da suka ji rauni domin yi musu fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

Ya ba su tabbacin cewa hukumar za ta yi amfani da duk wata hanya da take da ita kuma za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin gano waɗanda ke da alhakin kai musu harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI
  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 8 Kan Zargin Kashe Jariri A Borno
  • An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar Chadi
  • An buɗe wa jami’an NDLEA wuta a Abuja
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa