Sojojin Najeriya Sun Yi Jana’izar Bangirma Ga Wani Doki A Kaduna
Published: 28th, January 2025 GMT
Runduna daya ta sojojin Najeriya ta gudanar da bikin jana’izar marigayi Mascot, Sajan Dalet Danfari Akawala, a shalkwatar rundunar dake jihar Kaduna. Wanda dokin sojojin ne.
A wata sanarwa da mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya ya fitar, ya ce Kanar Akabike ne ya jagoranci jana’izar, wanda ya wakilci babban hafsan rundunar, Manjo Janar Mayirenso Lander David Saraso.
A cewar sa, Marigayi Sajan Dalet Danfari Akawala ya yi hidimar sashen sadaukarwa da aminci, tare da nuna jajircewa da juriya a gidan Soja.
“Bikin shi ne hanyar mu na girmamawa ta ƙarshe ga wani wanda ya kawo sauyi da farin ciki da aiki tukuru da kuma daukaka sashen da yayi aiki”
Kanar Akabike ya mika ta’aziyyarsa ga daukacin wadanda sukayi aiki da shi da sojojin Najeriya, yana mai nuna jimami game da wannan rashin da aka yi.
Ya kuma yabawa manyan baki da masu jajantawa da suka halarci bikin, yayin da aka yi addu’o’in Allah ya ba shi jajircewa, gwargwado, da kwazon maye gurbin marigayi Sajan Akawala.
A yayin bikin jana’izar, an bayyana Sajan Akawala a matsayin wanda ya fito daga zuriyar Mascot na Sashen, Sajan Farin Doki, wanda ya yi aiki daga 1995 har zuwa rasuwarsa a shekarar 2011. Bayan rasuwar Sgt Farin Doki, rundunar ta samu sabon mascot, Sgt Danfari. Akawala, wanda ya yi aiki har zuwa rasuwarsa a shekarar 2014. Sgt Danfari Akawala’s foal, Sgt Dalet.
An kammala jana’izar ne da addu’o’i da mukaddashin Daraktan (Protestant), Laftanar Kanal Ugwu ya yi, kuma ya samu halartar manyan hafsoshi, sojoji da iyalansu.
PR/Usman Sani/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Janar Sari: Sojojinmu Sun Yi Taho Mu Gama Da Amurkawa Sau 3 A Cikin Sa’o’i 24
Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sari ya sanar da cewa sau uku su ka yi taho mu gama da sojojin da suke cikin jirgin dakon jirayen yakin Amurka “ Trauman” a cikin sa’oi 24.
A wata sanarwa da janar Yahya Sari ya yi a jiya Asabar ya bayyana cewa; Sun kai wa jirgin dakon jiragen yakin na Amurka da kuma sauran jiragen da suke ba shi kariya a cikin tekun “Red Sea”.
Kakakin sojan na kasar Yemen ya kuma ce; Sun kai wa jiragen na Amuka hare-hare ne da jiragen sama marasa matuki da kuma makamai masu linzami mabanbanta.
An shiga makwanni na uku kenan da sojojin na Yemen suke mayar da martani akan hare-haren da sojojin Amurka da Birtaniya suke kai wa kasarsu.
Kasar ta Yemen tab akin jagororinta za su ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare har zuwa lokacin da za a daina yaki da Gaza da kuma dauke takunkumin da aka akakaba wa zirin na hana shigar da kayan agaji.
Baya ga kai wa Amurka da Birtaniya da sojojin na Yemen suke yi, suna kuma hana duk wani jirgin ruwa ratsawa ta tekun “Red Sea” matukar zai nufi HKI.
Sa’o’i kadan da su ka gabata ma dai sojojin kasar ta Yemen sun harba makamai masu linzami zuwa HKI