Aminiya:
2025-04-02@01:27:59 GMT

Gaskiyar batun kama Bello Turji —Sojoji

Published: 28th, January 2025 GMT

Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya ta yi tsokaci a karon farko kan  labarin da ke yawo cewa sojojinta sun kama ƙasurgumin ɗan ta’adda, Bello Turji.

Rundunar tsaron ta sanar da gaskiyar lamarin ne bayan raɗe-raɗin kama Bello Turji ya karaɗe kafofin sada zumunta.

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro, Manjo-Janar Edward Buba, ya sanar cewa babu ƙamshin gaskiya a labarin kama Turji, amma suna neman shi ruwa a jallo.

A jawabinsa ga ’yan jarida, Edward Buba ya shawarci ’yan Najeriya su yi watsi da labarin ƙaryan, da cewa, “duk labarin da ake bazawa game da kama Bello Turji ƙanzon kurege ne.”

Tun bayan da sojoji suka tsananta ragargazar sansanonin ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, musamman Jihar Zamfara inda ya fi yin ɓarna, aka daina jin ɗuriyarsa.

A makon jiya sojoji suka kashe ɗan Bello Turji, da manyan yaran ɗan ta’addan, ciki har da babban mataimakinsa da manyan kwamadoninsa bakwai.

Bello Turji na daga cikin manyan ’yan ta’addan da a tsawon shekaru suka addabi jihohin Zamfara da Katsina da Sakkwato da Kaduna da Kebbi da hare-hare inda suke yi wa jama’a kisan gilla tare da garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa da sace dabbobi da ƙona dukiyoyi.

A yayin da jami’an tsaro ke faɗi-tashin murƙushe su, lamarin ya sake ɗaukar sabon salo bayan ɓullar wata sabuwar ƙungiyar ’yan ta’addan ƙasashen waje, wadda aka fi sani da Lakurawa, musamman a jihohin Sakkwato da Kebbi.

Aƙalla shekara goma ke nan da ’yan bindiga suka addabi yankin Arewa maso Yamma, inda suka rabba dubban ɗaruruwan mutane da garuruwansu, suka hana harkokin noma da kasuwanci, baya ga karɓar daruruwan miliyoyi a matsayin kuɗin fansa ko haraji da suka ƙaƙaba ba al’umma.

Ko a kwanakin baya, wasu labarai sun yi yawo a kafofin sada zumunta cewa dakarun sojin ƙasar Jamhuriyar Nijar sun kama Bello Turji bayan da sojojin Najeriya suka fatattaki shi. Amma daga baya ta bayyana cewa labarin shaci-faɗi ne.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Edward Buba Sakkwato Tsaro Turai Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina

Iyayen Abdulsalam Rabi’u Faskari, wanda aka sace tare da mahaifinsa a Jihar Katsina, sun bayyana cewa sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Abdulsalam, wanda ya lashe gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa da aka gudanar a Jihar Kebbi, an sace shi tare da mahaifinsa da wasu makonni biyu da suka gabata, bayan Gwamnan Katsina ya karrama shi.

Talakawa su girmama shugabanni yayin bayyana matsalolinsu — Sarkin Musulmi. Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Mahaifinsa, Malam Rabiu Zakariya Faskari, ya shaida cewa suna tsare a hannun ’yan bindiga a Katsina har sai da wani babban ɗan bindiga mai suna Yellow daga Zamfara ya zo ya karɓe su da ƙarfi.

“Ya yi wa masu garkuwa duka kafin ya tafi da mu,” in ji shi.

Ya ce an yi ciniki kan fansa amma Yellow ya ƙi yarda.

“Muna ta addu’a har ranar Juma’a da aka zo aka ce mu fito mu tafi. Yaransa suka ɗauke mu suka kai mu wani gari, daga nan muka yi tafiyar awa huɗu kafin muka samu mota.”

Malam Rabiu, ya ce da suka hau babur sai direban ya shaida musu cewa an kashe Yellow.

“Ashe mutuwarsa ce ta sa yaransa suka sake mu muka koma gida.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Kisan Mafarauta: Matakan da gwamnatin Edo da ta Kano suke ɗauka
  • Yadda ‘Yan Banga A Edo Suka Yi Sanadin Kashe Matafiya Mafarauta 16 – Direban Motar
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Gwarzon gasar Alƙur’ani ya Kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • Miji ya kama matarsa da kwarto ta na’urar drone
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu