‘Yan Tawayen Sudan Sun Kona Wani Bangaren Matatar Mai Ta Al-Jili Da Ke Birnin Khartoum Bahri
Published: 28th, January 2025 GMT
Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Kungiyar Rapid Support Forces sun kai hari kan matatar mai ta Al-Jili da ke birnin Khartoum na kasar Sudan
Mayakan kungiyar dakarun kai daukin gaggawa sun kai hari kan matatar mai ta Al-Jili da ke birnin Khartoum Bahri, wadda ita ce matatar mai mafi girma a kasar Sudan, wadda take samar da man fetur a yawancin jihohin kasar ta Sudan, duk kuwa da cewa kwararru sun tabbatar da takaitar barnar da aka yi wa matatar Man duk da tashin bam da aka samu a cikin matata da ya tilasta dakatar da duk wani aiki a cikinsa.
Sojojin Sudan sun yi amfani da dama a lokacin da dakarun kungiyar Rapid Support Forces suke fita daga matatar man, zuwa shiyar lardin Darfur domin neman mafaka mafi aminci, inda sojojin suka yi musu luguden bama-bamai ta hanyar jiragen saman yaki, wasu rahotonni suna cewa; Har yanzu Dakarun kai daukin gaggawan ne suke iko da mafi yawan jihohin lardin Darfur da ke arewacin kasar ta Sudan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta bada rahoton cewa sojojin HKI sun kashe akalla yara 16 tun farkon wannan shekara ta 2025 a yankin yamma da kogin Jordan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ayed Abu Eqtaish, daraktan kungiyar ‘ The Defense for Children International’ a yankin yamma da kogin Jordan yana fadar haka. Ya kuma zargi manya manyan kasashen duniya da kyale gwamnatin HKI tana aikata irin wadannan laifuka kan Falasdinawa a gaban idan kowa.
Eqtaish ya kara da cewa, rashin magana da kuma takawa gwamnatin yahudawan birki yana sa ta kara yawan kashe yara Falasdinawa a duk sanda ta ga dama.
Kafin haka wani rahoton MDDya bayyana cewa idan ba’a hana HKI da karfi ba, to ba za ta takaita kisan kiyanshi a Gaza kadai ba, zata fadadashi zuwa yankin yamma da kogin Jordan.
Sojojin HKI sun ta aikata kissan kiyashi a gaza a yain fin karfin da ta yi a Gaza na tsawon watanni 15, inda ta kashe fal;asdinawa fiye da 61,000 kafin a tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Jenerun da ya gabata.