Sanatan Amurka Ya Yi Kakkausar Suka Kan Batun Tilastawa Falasdinawa Yin Gudun Hijira Daga Gaza
Published: 28th, January 2025 GMT
Dan Majalisar Dattawan Amurka ya bayyana kiran da shugaban Amurka ya yi tilastawa Falasdinawa gudun hijira Falasdinawa da cewa kokari ne na shafe wata al’umma daga kan doron kasa
Dan Majalisar Dattawan kasar Amurka Sanata Bernie Sanders a jiya Litinin ya fara mayar da martani ga shugaban Amurka Donald Trump inda ya bayyana kiran da Trump ya yi na korar Falasdinawa daga Zirin Gaza zuwa kasashen da ke makwabtaka da su a matsayin kokarin “Shafe wata al’umma ce daga kan doron kasa kuma laifin yaki ne” inda ya bukaci dukkan Amurkawa da su yi Allah wadai da wannan furuci.
A ranar Asabar da ta gabata ce shugaban Amurka Donald Trump ya ba da shawarar mayar da Falasdinawa daga zirin Gaza zuwa kasashen da suke makwabta da su kamar Masar da Jordan, yana mai cewa Zirin Gaza ba wuri ne da ya dace da zamansu ba, sakamakon kisan kiyashin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi musu.
Sanders ya ce: “Dole ne duk wani Ba’amurke ya yi Allah wadai da wannan mugun ra’ayi na Trump na korar Falasdinawa daga tushensu,” yana mai jaddada cewa: Kiran da Trump ya yi na tilastawa miliyoyin Falasdinawa kaura daga Gaza zuwa kasashe makwabta yana da sunan da ya dace da shi: wato “shafe wata kabilanci daga tushe karkashin laifin yaki.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Falasdinawa da
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
An tabbatar da rasuwar mutum uku tare da asarar gonakin shinkafa da faɗinsu ya kai hekta dubu 10 a Jihar Neja a sakamakon mummunar ambaliyar ruwa.
Wannan ibtila’i ya faru ne a Ƙaramar Hukumar Mikawa, sakamakon sakin ruwa daga Madatsar Ruwa ta Jebba.
Shaidu sun bayyana cewa ambaliyar ta yi ɓarna sosai a gonakin yankin.
Shugaban Ƙungiyar Raya Yankin Kede, Abdulraham Abdulƙadir Kede-Wuya, ya ce gonar shinkafarsa mai faɗin hekta uku na daga cikin waɗanda suka salwanta a ambaliyar.
Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno An shiga ruɗani kan satar al’aurar maza a ƙasar ChadiYa ce, “gonata mai faɗin hekta uku na daga cikin waɗanda ruwan ambaliyar ya shanye, Sannan akwai sauran masu gonaki. Duk gonakin da bain ya shafa sun kai lokacin girbi. Ba mu san abin da ya da suka saki ruwan a irin wannan lokaci ba tare da sanar da al’umma ba.”
Wani manomi a yankin, Ibrahim Ndako, ya bayyana ambaliyar a matsayin bala’i, yana mai kira ga hukumomi su kawo musu ɗauki.
Ibrahim ya bayyana cewa, “Irin asarar asarar rayuka da maƙudan kuɗaɗe da wahalhalun da manoman rani suka tafka a sakamakon wannan abu, da wuya a iya mayar da shi.”
Ya ce yawancin manoma sun zo yankin ne daga jihohi Kebbi, Sakkwato, Zamfara Kano da Borno, domin yin noman rani a yankin, amma yanzu an jawo musu asarar.
Aminiya ta samu labarin cewa wasu daga cikin manoman sun fara girbi a lokacin da ambaliyar ta auku.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Daraktan Yaɗa Labarai na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Ibrahim Aufu Hussaini ya ce an samu asarar rayukan ne a lokacin da wani kwalekwale ɗauke da su yake ƙoƙarin tsallake kogi da su bayan ambaliyar.
Ya bayyana cewa hukumar tana ci gaba da bincike domin tantance girman asarar da aka yi a sakamakon ambaliyar.