Dan Majalisar Dattawan Amurka ya bayyana kiran da shugaban Amurka ya yi tilastawa Falasdinawa gudun hijira Falasdinawa da cewa kokari ne na shafe wata al’umma daga kan doron kasa

Dan Majalisar Dattawan kasar Amurka Sanata Bernie Sanders a jiya Litinin ya fara mayar da martani ga shugaban Amurka Donald Trump inda ya bayyana kiran da Trump ya yi na korar Falasdinawa daga Zirin Gaza zuwa kasashen da ke makwabtaka da su a matsayin kokarin “Shafe wata al’umma ce daga kan doron kasa kuma laifin yaki ne” inda ya bukaci dukkan Amurkawa da su yi Allah wadai da wannan furuci.

A ranar Asabar da ta gabata ce shugaban Amurka Donald Trump ya ba da shawarar mayar da Falasdinawa daga zirin Gaza zuwa kasashen da suke makwabta da su kamar Masar da Jordan, yana mai cewa Zirin Gaza ba wuri ne da ya dace da zamansu ba, sakamakon kisan kiyashin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi musu.

Sanders ya ce: “Dole ne duk wani Ba’amurke ya yi Allah wadai da wannan mugun ra’ayi na Trump na korar Falasdinawa daga tushensu,” yana mai jaddada cewa: Kiran da Trump ya yi na tilastawa miliyoyin Falasdinawa kaura daga Gaza zuwa kasashe makwabta yana da sunan da ya dace da shi: wato “shafe wata kabilanci daga tushe karkashin laifin yaki.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Falasdinawa da

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga

Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC), Manjo Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya kuɓuta bayan shafe kwana 22 a hannun ’yan bindiga.

An sace shi ne a ranar 6 ga watan Fabrairu, 2025, a gidansa da ke garin Tsiga a Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina, yayin da wasu ’yan bindiga suka kai hari.

Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250 Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta

Maharan sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 250 kafin su sako shi.

Sai dai bayan tattaunawa, an biya kuɗin fansa, wanda ya kai ga sakinsa.

A halin yanzu, likitoci na kula da shi a wani asibiti da ba a bayyana ba sunansa ba.

A lokacin kai harin, sama da ’yan bindiga 100 ne suka afka gidansa, suka yi awon gaba da shi da wasu mazauna yankin.

Wasu mutum biyu sun samu raunuka yayin harin, yayin da wani daga cikin ’yan bindigar ya harbi ɗan uwansa bisa kuskure, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Har yanzu, rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ba ta fitar da wata sanarwa kan sakin tsohon shugaban NYSC ɗin ba.

Satar mutane da hare-haren ‘yan bindiga na ci gaba da zama babbar barazana ga tsaro a Jihar Katsina da sauran sassan Najeriya.

Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro na fuskantar matsin lamba wajen shawo kan wannan matsala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Sami Tarba Mai Kyau A Burtaniya Bayan Cacan Baki Mai Zafi Da Trump
  • Motocin Buldoza Suna Ta Rusa Gidajen Falasdinawa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • Al-Houthi : Isra’ila Na fakewa Da Goyan Bayan Amurka Tana Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
  • Gobara ta hallaka mutum 2 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta
  • Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da ‘yanci daga wuta