Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Zai Gana Da Jami’an Iran Da Jakadojin Kasashen Musulmi
Published: 28th, January 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran zai karbi bakwancin tawagar jami’an kasar da jakadun kasashen musulmi
A cikin sa’o’i masu zuwa ne Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zai karbi bakwancin wasu tawagogin jami’an kasar, baya ga wakilai da jakadun kasashen musulmi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa: Wannan taro ya zo ne domin murnar tunawa da zagayowar ranar aiko fiyayyen halitta, Manzon Tsira Muhammadu dan Abdullahi (s.a.w) da sakon addinin Musulunci ga dukkan talikai wanda ya yi daidai da yau Talata 28 ga watan Janairu, kuma daidai da ranar 27 ga watan Rajab shekara ta 1446 bayan hijira.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya taya al’ummar Musulmi murna bisa kammala azumin watan Ramadan lafiya, tare da kira garesu da su rungumi koyarwar Annabi Muhammadu (S.A.W) a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.
Ya bayyana hakan ne a sakon sa na Sallah ga al’ummar jihar.
Malam Umar Namadi ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da ya karɓi azumi da addu’o’in al’ummar Musulmi da suka yi a watan na Ramadan.
Haka kuma, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya ci gaba da yi wa shugabanni jagorancin don yin abin da ya dace domin jin daɗin al’umma.
Namadi ya kuma yi addu’ar samun zaman lafiya, da hadin kai, da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.
Radiyon Najeriya ya ruwaito cewa, Gwamnan ya kuma karɓi manyan baki da suka kai masa gaisuwar Sallah a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Usman Muhammad Zaria