Aminiya:
2025-04-24@23:20:44 GMT

A soma duba watan Sha’aban ranar Laraba — Sarkin Musulmi

Published: 28th, January 2025 GMT

Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III ya buƙaci al’ummar Musulmi da su fara duba sabon watan Sha’aban na kalandar musulunci daga daren Laraba.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bayar da shawara kan harkokin addini a fadar, Farfesa Sambo Wali Junaidu, ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Gaskiyar batun kama Bello Turji —Sojoji Kotu ta hana ’yan sanda sake taɓa Muhuyi Rimingado 

Kwamitin ganin wata na Nijeriya a Fadar Sarkin Musulmi ya ce ranar Laraba ce za ta zama 29 ga watan Rajab, 1446, daidai da 29 ga watan Janairun 2025.

Sanarwa da Fadar Sarkin Musulmin ta fitar, ta ce idan aka ga watan a kai rahoto zuwa ga hakimi ko kuma mai unguwa mafi kusa wanda shi kuma zai sanar da fadar.

Watan Sha’aban dai yana da muhimmanci a kalandar Musulunci, saboda daga shi ne za a shiga watan azumin Ramadan.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fadar Sarkin Musulmi Jinjirin Wata Sarkin Musulmi Watan Sha aban Sarkin Musulmi

এছাড়াও পড়ুন:

Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da ƴan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Rwanda sun amince su dakatar da faɗa a gabashin ƙasar har sai an kammala tattaunawar sulhu da ke gudana a halin yanzu wanda Qatar ke shiga tsakani.

Wannan dai ita ce yarjejeniyar sulhu ta baya-bayan nan tun bayan da ƴan tawayen suka ƙara kai farmaki a gabashin ƙasar inda hukumomi suka ce an kashe mutane 7,000 tun daga watan Janairu.

A ranar Larabar da ta gabata ce, ɓangarorin biyu suka ba da sanarwar yin aiki tare don samar da zaman lafiya, bayan shafe sama da mako guda suna tattaunawa, wanda suka ce an gudanar cikin aminci tare da mutunta juna.

A watan da ya gabata, shugaban ƙasar Congo Félix Tshisekedi da takwaransa na Rwanda Paul Kagame suma sun jaddada aniyarsu ta tsagaita wuta ba tare da sharaɗi ba a wata ganawar ba-zata da suka yi a birnin Doha.

Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana gwabzawa ya ƙara kamari ne a watan Janairu, lokacin da ƙungiyar M23 ta ƙaddamar da wani farmaki da ba a taɓa ganin irinsa ba, inda ta ƙwace garuruwan Goma da Bukavu – manyan biranen ƙasar Congo guda biyu, lamarin da ya haifar da fargabar ɓarkewar yaƙi yankin baki ɗaya.

DR Congo na zargin Rwanda da bai wa ƙungiyar M23 makamai tare da tura dakaru domin tallafawa ƴan tawayen.

Duk da ikirarin da Majalisar Dinkin Duniya da Amurka suka yi, Rwanda ta musanta zargin da ake yi ma ta na goyon bayan ƙungiyar M23.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Baffa Bichi, Kabiru Rurum, Sha’aban Sharada Da Wasu Sun Koma Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB
  • Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • An Umurci Sojoji Su Kawarda ‘Yan Bindiga Daga Kwara Da Niger A Cikin Wata Daya
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran