Aminiya:
2025-04-02@22:00:38 GMT

A soma duba watan Sha’aban ranar Laraba — Sarkin Musulmi

Published: 28th, January 2025 GMT

Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III ya buƙaci al’ummar Musulmi da su fara duba sabon watan Sha’aban na kalandar musulunci daga daren Laraba.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bayar da shawara kan harkokin addini a fadar, Farfesa Sambo Wali Junaidu, ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Gaskiyar batun kama Bello Turji —Sojoji Kotu ta hana ’yan sanda sake taɓa Muhuyi Rimingado 

Kwamitin ganin wata na Nijeriya a Fadar Sarkin Musulmi ya ce ranar Laraba ce za ta zama 29 ga watan Rajab, 1446, daidai da 29 ga watan Janairun 2025.

Sanarwa da Fadar Sarkin Musulmin ta fitar, ta ce idan aka ga watan a kai rahoto zuwa ga hakimi ko kuma mai unguwa mafi kusa wanda shi kuma zai sanar da fadar.

Watan Sha’aban dai yana da muhimmanci a kalandar Musulunci, saboda daga shi ne za a shiga watan azumin Ramadan.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fadar Sarkin Musulmi Jinjirin Wata Sarkin Musulmi Watan Sha aban Sarkin Musulmi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Watan azumin Ramadana kan zo da sauye sauye da dama da suka haɗa da ƙara ƙaimi wajen bauta wa ubangiji, samun lada ta hanyar ciyar da al’umma da kuma falala masu yawa da ba su misaltuwa.

Wani sauyi da watan azumin watan Ramadana ke zuwa da shi shi ne canjin yanayin cimar al’umma, inda mutane ke canzawa daga cin abinci sau uku ko sama da haka a rana zuwa sahur da kuma buɗe-baki.

Bayan kwanaki 29 zuwa talatin na samun waɗannan canji, ta waɗanne hanyoyi ne al’umma za su koma cimaka kamar yadda suka saba gabanin watan Ramadana

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Kafin Da Kuma Ranar Sallah DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah

Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan hanyoyin da mutum ya kamata ya bi don komawa cin abinci yadda ya kamata bayan azumtar watan Ramadana.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Arewa Ke Tafiya Kudu Farauta
  • BUK Ta Ƙaddamar Da Shafin Intanet Da Ɗalibai Za Su Ke Duba Sakamakon Jarrabawa
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Muna jiran ganin hukuncin da za a ɗauka kan kashe ’yan Arewa a Edo — Sarkin Musulmi
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya