A soma duba watan Sha’aban ranar Laraba — Sarkin Musulmi
Published: 28th, January 2025 GMT
Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar III ya buƙaci al’ummar Musulmi da su fara duba sabon watan Sha’aban na kalandar musulunci daga daren Laraba.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bayar da shawara kan harkokin addini a fadar, Farfesa Sambo Wali Junaidu, ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.
Kwamitin ganin wata na Nijeriya a Fadar Sarkin Musulmi ya ce ranar Laraba ce za ta zama 29 ga watan Rajab, 1446, daidai da 29 ga watan Janairun 2025.
Sanarwa da Fadar Sarkin Musulmin ta fitar, ta ce idan aka ga watan a kai rahoto zuwa ga hakimi ko kuma mai unguwa mafi kusa wanda shi kuma zai sanar da fadar.
Watan Sha’aban dai yana da muhimmanci a kalandar Musulunci, saboda daga shi ne za a shiga watan azumin Ramadan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fadar Sarkin Musulmi Jinjirin Wata Sarkin Musulmi Watan Sha aban Sarkin Musulmi
এছাড়াও পড়ুন:
Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp