Aminiya:
2025-04-24@19:13:43 GMT

Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco

Published: 28th, January 2025 GMT

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka CAF, ta fitar da jadawalin ƙasashen da za su fafata a Gasar Kofin Nahiyyar Afirka AFCON wadda Morocco za ta karɓi baƙunci a watan Disamba na bana.

An gudanar da bikin fitar da jadawalin ranar Litinin a Cibiyar Taro ta Ƙasa ta Mohammed V National da ke birnin Rabat a Morocco.

A soma duba watan Sha’aban ranar Laraba — Sarkin Musulmi Nijeriya na da arzikin da za ta riƙa ɗaukar nauyin tafiye-tafiyen Tinubu — Minista

Tawagogi biyu mafi ƙwazo a kowanne rukuni ne za su tsallaka kai tsaye zuwa mataki na gaba, sai kuma tawagogi huɗu mafi ƙwazo da suka zo a mataki na uku a duk cikin rukunan.

Morocco wadda wannan shi ne karo na farko da za ta kasance mai masaukin baƙi tun 1988, za ta jagoranci rukunin A, inda za ta ɓarje gumi da Mali da Zambia da kuma Comoros.

Masar da ta taɓa lashe gasar sau bakwai a tarihi, za ta kara ne da Afrika ta Kudu da Angola da kuma Zimbabwe a rukunin B.

Rukunin C kuwa wanda ya ƙunshi Nijeriya wadda ta lashe kofin sau uku, za ta yi karon-batta da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania.

Senega da ta lashe gasar a shekarar 2021, za ta kara da Jamhuriyar Dimukaraɗiyar Congo da Benin da kuma Botswana wacce wannan ne karo na biyu da za ta halarci gasar.

Algeria ce ke jagorantar rukunin E wanda ya ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Equatorial Guinea da Sudan.

Cote d’Ivoire wacce ke kare kambin ta na rukuni F, tare da Kamaru da Gabon da kuma Mozambique.

A dai ranar 21 ga watan Disamba ne za a buɗe gasar da karawa tsakanin Morocco da Comoros, sai kuma a buga wasan ƙarshe a ranar 18 ga watan Janairun 2026.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba

Kujeru dubu daya da dari hudu da bakwai ne aka ware wa hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Taraba domin maniyyata bana.

 

Babban Sakataren Hukumar mai barin gado Umar Ahmed Chiroma ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan matakin da ake na shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana na 2025 ba tare da tangarda ba.

 

Aikin Hajji daya ne daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar kuma Musulmin muminai na gudanar da aikin Hajji a kowace shekara akalla sau daya a rayuwarsu.

 

Chiroma ya ce hukumar ta kai wani mataki na ci gaba ta fannin shirye-shirye kamar yadda hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta bayar, inda ya ce sama da maniyyatan jihar 500 ne suka kammala biyan kudadensu.

 

Alhaji Ahmed Umar Chiroma ya kara da cewa a halin yanzu sama da Alhazai dubu biyar ne suka biya kudin aikin Hajji, yana mai kira ga sauran maniyyatan da su gaggauta biya domin cika wa’adin da hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kebe.

 

Ya yi bayanin cewa hukumar ta samu karancin masu zuwa aikin hajjin ba, inda ya danganta hakan ga tabarbarewar tattalin arziki ganin yadda amfanin gona da shanu suka ragu matuka a farashi.

 

Sakataren zartarwa ya bayyana manoma da makiyaya a matsayin manyan masu biyan kujerun aikin Hajji a jihar, inda ya nuna cewa gwamnatin jihar ta biya kujeru hamsin (50).

 

Chiroma ya ci gaba da bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara yin alluran rigakafi da tantance maniyyatan da ke shirin kammala shirye-shiryen aikin Hajji.

 

A cewarsa, hukumar ta kammala shirye-shirye a sansanin Alhazai a Jalingo, babban birnin jihar.

 

Sakataren zartarwa mai barin gado ya bayyana karara cewa jami’an hukumar sun ziyarci kasar Saudiyya inda suka samu masaukin da suka dace da mahajjatan jihar Taraba.

 

Umar Ahmed Chiroma ya yabawa Gwamna Agbu Kefas bisa daukar nauyin Alhazai hamsin, yana mai jaddada cewa wannan karimcin zai taimaka matuka wajen taimakawa mutane da dama wajen gudanar da aikin hajjin 2025.

 

 

Sani Sulaiman

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Hajjin 2025: Sahun Farko Zai Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki 9 Ga Watan Mayu
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • Burnley Da Leeds United Sun Dawo Gasar Firimiya Lig