Aminiya:
2025-04-23@15:49:25 GMT

Sojoji sun ƙwato tarin makamai a Zamfara

Published: 28th, January 2025 GMT

Dakarun rundunar Operation Fansar Yamma sun ce sun ƙwato tarin makamai a Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda na Jihar Zamfara.

Dakarun tare da haɗin gwiwar jami’an tsaron farin kaya (DSS), sun kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan masu safarar makamai daga Jamhuriyar Nijar zuwa Najeriya.

Tankar mai ta sake fashewa a Neja Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran rundunar, Laftanar-Kanal Abubakar Abdullahi ya fitar, ya ce sun ƙaddamar da farmaki ranar 27 ga watan Janairun 2025, abin da ya kai ga ƙwato makaman kan hanyar Namoda zuwa Zurmi.

Ya ce waɗanda ake zargin sun tsere zuwa cikin daji tare da barin motarsu bayan artabu da sojoji.

Kanal Abubakar ya ce bayan binciken da suka yi a cikin motar, sun gano makamai da dama da suka haɗa da bindigar AK-47 guda tara da harsasai daban-daban.

A ɗaya gefen, dakarun sun ce sun baza koma domin cafke ƙasurgumin ɗan bindigar nan Bello Turji wanda ake nema ruwa a-jallo.

Bayanai sun ce Turji na ci gaba da guje-guje da sojoji daga maɓoya zuwa maɓoya.

Dakarun sun tabbatar da cewa suna aiki tuƙuru domin kama Turji da zummar dawo da zaman lafiya a al’ummomin da suka addaba da hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakaru Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Zai Dawo Nijeriya A Yau Litinin Bayan Ziyarar Aiki A Turai

Shugaba Tinubu ya bar Nijeriya ne a ranar 2 ga watan Afrilu zuwa birnin Paris na kasar Faransa, domin wata ‘yar gajeriyar ziyarar aiki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • Iran Zata Gudanar Da Tarin Kare Hakkin Bil’adama Ta Faskar Gabacin Duniya A Karo Na Farko
  • Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta
  • Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Boko Haram A Yobe
  • Shugaba Tinubu Zai Dawo Nijeriya A Yau Litinin Bayan Ziyarar Aiki A Turai
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • Sojojin Lebanon Sun Kama Wasu Mutanen Da Suke Shirin Cilla Makamai Kan HKI