Tashe-Tashen Hankula A Birnin Kinsshsa Na Democradiyyar Kongo Da Kuma Kwasar Ganima
Published: 28th, January 2025 GMT
Bayan hare haren da mutane suka kai kan ofisoshin jakadancin kasashen Ugandan, Rwandan, Kenyan, Japan, Amurka da kuma Faransa a birnin Kinshasa na kasar Democradiyya Congo masu zamga-zanga sun fara kwasar ganima a manya-manyan shaguwa a birnin.
Masu zanga-zangar sun fara tada hankali a kasar ne saboda irin saurin ci gaban da yan tawayen M23 suke mamayar kasar.
Labarin ya kara da cewa an ga hayaki na tashi a ofishin jakadancin kasar Faransa a Kinshasa, kuma suna yin haka ne don nuna turjiya ga halayen mulkin mallaka na kasar faransa, wacce take daga cikin wadanda suke goyon bayan yan ta’addan.
A kwanakin da suka gabata dai kungiyar M23 dauke da makamai cikin kungiyoyi fiye da 100 dauke da makamai a arewacin yankin KIVU a DMC mai arzikin ma’adinan da ake bukatarsu a manya-manyan kamfanoni a duniya, ta kwace yankuna da dama daga ciki har da birnin goma babban birnin lardin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan Almujtaba (a) 110
110- Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatana masu sauraro zasu kasance tare da mu.
///.. Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).
Idan kuna tare da mu, masu sauraro a cikin shirimmu da ya gabata, mun yi cikekken bayani dangane da rayuwar Abdullahi dan Abi sarkh, wanda ya Khalifa Uthman ya sanya wali ko gwamna a kan mutanen kasar Masar, da kuma yadda suka kai kararsa wajen Khalifa, amma Khalifa ya rubuta wasiya ya ja kunnensa, sannan ya bukaci ya sauya halayensa, amma ba wai kawai ya ki sauya halayensa ba sai dai ya kashe wanda ya kai kararsa gaban Khaliga.
A nan su mutanen kasar Masar suka fusata suka tura mutane 700 zuwa madina inda suka nemi shawarar wasu daga cikin sahbban manzon All..(s), daga ciki har da Aliyu dan Abitalib (s) wanda ya shiga wajen Khalifa ya yayi masa magana, kuma ya amince ya sauya masu gwamnansu, sai yace su zabi wanda suke so, sai suka zabi Muhammad dan Abubakar.
Mun kuma bayyana yadda aka haifeshi a hajjin bankwana, kuma yana dan watanni 3 a duniya manzon All..(s) ya kauracewa duniyar, sannan baya rasuwar Khalifa a Abubakar, yana mai yuwa dan shekara 3-4 mahaifiyarsa ta gama idda sai Amirulmuminina (a) ya aureta.
Don haka Muhammad dan Abubakar yana dan shekara kimani 26 a duniya khalifa Uthman ya sanyashi gwamnar Madina, amma abin mamaki shi ne sun isa wani gari ana kiransa Hums a kan hanyar masar sai suka gamu da wani bawan Uthman dauke da wasika daga wajensa zuwa wajen Abdullahi dan Abi sarkh, inda a ciki ya bukaci ya kashesu gaba daya har tare da sabon Gwamnan. Amma sun lura cewa rubutun hannun Marwan dan Hakam ne.
Daga nan sai suka kama wrsh bawan Uthman da kuma wasikar da suka samu a wajensa suka shiga madina. Suka nunawa Amirulmuminina wasikar, ya karbeta ya shiga wajen Uthman, sannan ya nuna masa wasikar ya kuma tambayeshi ko shi ne ya rubuta? Sai yace a’a, sai ya tambaye shi wa kake tuhuma, sai ye babu wanda yake tuhuma.
A nan ce sai ya koma gida ya kama gidansa ya kulle, don ya san cewa fitina zata auku.
Don haka mutanen masar sun yiwa gidan Khalifa a Madina Kawanya, babu wanda ya taimaka masa cikin dimban sahabban manzon All..(s), sun barshi da yan tawaye wadanda suka yiwa gidansa kawanya suka hana shigar ruwa da abinci cikin gidan.
Kafin mu dawo kan wannan, bari mu dubi yadda Khalifa Uthman ya wanye da Abdullahi dan Masaud daya daga cikin manya-manyan sahabban manzon All..(s), wanda kuma manzon All..(s) da kansa ya yabe shi so sai. Ance shi ne mutum wanda yafi kama da manzon All..(s) a shiriyarsa sa da shirunsa. Kuma manzon All.. (s) yana fada dangane da shi, (wanda yake farinciki ya karanta Al-kur’ani a asalinsa da kuma danyensa kamar yadda aka sauko da shi, to yayi karatu da irin karatun dan Mas’udu).
Sannan wasu mutane sun yabe shi a gaban Amirulmuminina (a) sai yace : {Ni ma zan fada dangane da shi kamar yadda suka fada, yana daga cikin wadanda suka fi kowa iya karatun Kur’ani, ya halatta abinda ya halatta,ya kuma haramta abinda ya haramta, malami ne a sanin addini, ya san sunnar manzon All..(s) , yana daga cikin wadanda wannan ayar ta sauka tana yabonsu,
{Waɗanda suka karɓa kira zuwa ga Allah da ManzonSa, daga bãyan cuta ta sãme su. Akwai wata lãda mai girma ga waɗanda suka kyautata yi daga gare su, kuma suka yi taƙawa.} Ali Imrani aya ta 172. Har ila yau yana daga cikin wadanda wannan ayar ta sauka.
{Kuma kada ka kõri waɗanda suke kiran Ubangijinsu sãfe da maraice, sunã nufin yardarSa, babu wani abu daga hisãbinsu a kanka, kuma babu wani abu daga hisãbinka a kansu, har ka kõre su ka kasance daga azzãlumai.} Al-Anam 52.
Lalle Abdullahi dan masaud yana daga cikin manya manyan musulmi a zamanin manzon All..(s) a wajen shiriya, da kyawawan ayyuka,da kamun kai, don rikonsa da addini ne ya sa Khalifa Umar ya turashi zuwa Kufa tare da Ammar dan Yasir, sannan ya rubutawa mutanen kufa wasika inda a cikinta yake fada masu, (Lalle ya tura Ammar dan Yasir gareku a matsayin shugaba, da kuma Abdullahi dan Masa’ud Malami kuma mataimaki, suna daga cikin zababbun daga cikin sahabban manzon All..(s), suna daga cikin wadanda suka je yakin Badar, ku yi koyi da su, ku yi biyayya a garesu, ku ji maganganunsu, da zancensu, hakiki na zabi Abdullah gareku a kan kaina).
Don haka Abdullahi dan masa’ud ya zauna a kufa a tsawon khalifan Umar dan Khaddabi, wato shekari kimani 10, yana karantar da mutane addini, yana sanar da su littafin All..T, yana sanar da su ilmin addinin musulunci, yana nuna masu hanya madaidaiciya, tare da wannan ya kasance ma’ajin kudaden gwamnati a kufa.
A lokacinda Al-amura suka koma ga khalifa Uthman, sannan ya aika Walid dan Uqbah a matsayin wali a Kufa ! sai sabani ya shiga tsakaninsa da shi, kamar yadda muka yi magana a kan Walida an Uqbah a baya, wanda ya tilasta masa ajiye aikinsa na ma’ajin baitul Malin musulmi a Kufa.
Sai ya zauna a kufa kadan daga bayan ya koma Madina, a lokacinda zai tafi, sai mutanen kufa suka raka shi har bayan gari, don girmama shi da kuma bakin cikin rabuwa da shi. Suna fada masa a lokacinda suke bankwana da shi: All..ya saka maka da Alkhairi, ka sanar da Jahilai, ka karfafa ilmin malamammu, ka koya mana karatun Al-kur’ani, ka koya mana addini, madallah da dan’uwa musulmi irinka, madallah da aboki.
Sai yayin bankwana da su, ya kuma hanyarsa zuwa Madina, a shigo birnin a lokacin Khalifa Uthman yana khudaba a kan membarin manzon All..(s), a lokacinda Khalifa ya hango shi sai yana fadawa mutane yana kuma nuna shi, yana cewa : Ku saurara hakiku mummunan dabba ta zo maku, …..
Shin yakamata a zagi sahabin manzon All..(s) wanda bai aikata wani laifi ba, sai sabanin da ya samu da Walid dan Ukba, Sabon walin kufa wanda ya kha’inci All..da manzonsa kuma Ayar Alkur’ani ta sauka ta kira shi Fasiki, kuma yake satar kudaden musulmi!?.
Sai Ibn Mas’ud ya mayar masa da cewa: Ba haka bane, sai dai ni sahabin manzon All..(s), a ranar Badar da kuma bai’ar ridwan}. A lokacinda suka ji martanin Abdullahi dan Masa’ud sai wasu da dama sun tashi suna kareshi a gaban Uktman, daya daga cikinsu ita ce Aisha matar manzon All..(s) tana cewa : Ya kai Uthman kana fadar haka ga sahabin manzon All…(s)?
Sai Uthman ya bada umurnin aka fitar da Abdullahi dan masa’ud da karfi da kuma wulakanci. Sannan daya daga cikinsu, wanda ake kira Abdullahi dan Zam’ah ya daga shi ya buga da kasa, wasu sun ce wani ne ba shi ba, sannan ya dake shi a kan kirjinsa ya kuma karya masa awazarsa.
A lokacinda Imam Ali (a) ya ga haka, ko kuma ya ji labarin abinda aka yiwa Abdullahi dan Masa’ud ya zabura ya tashi yana daga murya yana cewa {Ya kai Uthman, ta yaya zaka yi haka da sahabin manzon All..(s) don abinda Walid dan Ukba ya fada maka dangane da shi?}.
Sai Uthman yace: Ba don Walid na yi masa haka ba, sai na aiki Zabaidah dan Sult Alkindi zuwa Kufa, sai dan masa’ud ya ce masa: Jinin Uthman ya halatta. Sai Imam Yace: Ya halatta a kan Zubaidah yayi haka ba tare da tabbatar da amincensa ba?
Sai Imam ya dauki dan Masa’ud zuwa gidansa yana jinyarsa. Sai Uthman ya yankewa dan Masa’ud baya zuwa wajensa, sannan ya sa aka dakatar da bashi albashinsa, sai ba’a dabe ba, dan Masaud ya yi rashin lafiyan da ya yi wafati a cikinta.
A lokacinda Uthman ya ji labarin rashin lafiyansa, sai ya zo gidansa, ya zauna kusa da shi, yana ce masa, menene damuwarka? Sai ibn Masa’ud yace: Zunubi na.
Sai yace: Me kakeso, sai yace, rahamar Ubangiji na, sai yace: Ba zan kira makama likita ba? Sai yace: Likitan ne ya sa ni rashin lafiya. Sai yace: In bada Umrni a maka kudadenka?: Sai yace: Ka hanani a lokacinda neka bukatarsa, sai ka bani shi a lokacinda bana bukatarsa? Sai yace: Sai ba barshi ga yayanka! Sai yace: Arzikinsu na hannun All..!
Sai Uthman yace: Ka gafarta mani ya baban Abdurrahman, Sai ibn Ma’ud yace: Ina rokon All.. ya karbammani hakkina daga gareka. Sai Uthman ya tashi ya tafi ya manta da shi.
Sannan a lokacinda ya kusan Mutuwa sai ya yi wasiyya kada Uthman ya sallaci gawarsa, sannan ya bukaci abokinsa Ammar dan yasir yayi mansa sallah idan ya rasu. Sannan bayan rasuwarsa Ammar da sauran salihan bayi suka yi masa sallah sannan suka sanyashi a bakiyah. A lokacinda Khalifa ya ji, ya yi fushi, sai ammar yace masa , wasiyya yayi kada ka yi masa salla.