Gwamnatin kasar News Zealand ta fitar da sabbin sharudda ga yahudawan HKI masu neman Visar Shiga kasar, daga ciki sai sun bada tarihin aikin sojen da suka yi a cikin kasarsu.

Takaita irin yahudawan da zasu shiga kasashen duniya bayana yakin Gaza dai, zai sanya wani tunani a zukatan yahudawan HKI musamman wadanda suka shiga yakin Gaza suka kuma yi wa Falasdinawa kissan kare dangi.

Kungiyoyi masu goyon bayan falasdinawa kimani 50 ne suka shigar da kara suka korafin a kissan kiyashe a Gaza wanda sojojin HKI suka yi a cikin watanni 15 da suka gabata a kotuna daban daban a duniya.

Gwamnatin kasar New Zealand dai tana tunanin hana duk wani soja daga cikin sojojin HKI wanda ya aikata kisan kiyashi a Gaza shiga kasarta. Ya zuwa yanzu dai gwamnatin kasar New Zealan ta haka akalla soja guda daga cikin sojojin HKI saboda kasancewa cikin sojojin da suka yi yaki a Gaza.

Jaridar Haaretz ta HKI ta bayyana cewa an sami irin wadannan korafe korafen a gaban kotuna a kasashen  Afirka da Kudu, Sri Lanka, Belgium, Faransa, da kuma Brazil.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza

Wasu Falasdinawa sun yi shahada a cikan kwana na 35 a sabon yakin da yahudawan sahayoniyya suka sake daurawa kan Zirin Gaza

Sojojin gwamatin mamayar Isra’ila suna ci gaba da yakin kisan kiyashi a Zirin Gaza tun bayan sake ci gaba da yau tsawon kwanaki 35 da suka gabata, bayan da Fira minista Benjamin Netanyahu ya yi watsi da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, kuma yana gudanar da wannan ta’asa ne tare da goyon bayan siyasa da na sojan Amurka, sannan kungiyoyin kasa da kasa gami da gwamnatocin kasashe sun daukin matakin yin shiru da rashin gwada wani yunkurin kalubalantar wannan danyen aiki.

Cibiyar yada labaran Falasdinu ta watsa rahoton cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-hare da dama tare da rusa gidaje, gami da karfafa haramcin shigar kayan abinci ga Falasdinawa tun farkon watan Maris da ya gabata. Wannan ya kara janyo bullar masifar yunwar da al’ummar Zirin Gaza ke fuskanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
  • Yeman : Sojojin Amurka sun kai wani gagarumin farmaki kan lardunan Sanaa da Hudaidah
  • Amurka Ta Kaddamar Da Sabbin Hare-Hare Kan Garuruwan Sana’a, Sa’adah Da Al-Jawf Na Kasar Yemen
  • Sojojin Sudan Sun Kashe ‘Yan Tawayen Kasar Ciki Har Da Manyan Kwamandojinsu A Birnin El Fasher
  • Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran
  • Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu
  • Kasar Sin Ta Nemi Kasashen Duniya Su Taimaka Wa Libya Wajen Fita Daga Kangin Da Take Ciki
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Hare Hare Kan HKI Da Jiragen Yakin Amurka