A dai-dai lokacinda jijiyoyin wuya suke kara tashi tsakanin JMI ta kuma HKI, jami’an tsaron HKI sun kama daya daga cikin yan rahotomta sun tsare.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban hukumar gidajen radiyo da Talabijin ta kasar (IRIB), Peyman Jebelli yana fadar haka ya kuma  kara da cewa dan rahoton hukumar baya Gaza, yana cikin kasashen Falasdinu da aka mamaye ne.

Sannan hukumar ta fara kokarin ganin an sake shi.

Labarin ya kara da cewa tun ranar da aka fara yakin tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 jami’an tsaron HKI sun kashe yan jaridu 205, sannan ta kama wasu 75, sannan har yanzun wasu 42 kuma tana tsare da su. Annan akalla 10 daga cikinsu tana tsare da su ne a karkashin dokannan da ake kira (administration datentiomn) wato tsarewa karkashin dokar masu iko.

Bisa bangare na 79 karkashin doka ta taron Geneva, yan jaridu wadanda suke aiki a cikin wurare masu hatsari su abin karewane kamar yadda ake bukatar a kare fararen hula, matukar basu dauki bangare a rikicin ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga

Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Matasa Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC), Manjo Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), ya kuɓuta bayan shafe kwana 22 a hannun ’yan bindiga.

An sace shi ne a ranar 6 ga watan Fabrairu, 2025, a gidansa da ke garin Tsiga a Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina, yayin da wasu ’yan bindiga suka kai hari.

Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250 Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta

Maharan sun nemi kuɗin fansa Naira miliyan 250 kafin su sako shi.

Sai dai bayan tattaunawa, an biya kuɗin fansa, wanda ya kai ga sakinsa.

A halin yanzu, likitoci na kula da shi a wani asibiti da ba a bayyana ba sunansa ba.

A lokacin kai harin, sama da ’yan bindiga 100 ne suka afka gidansa, suka yi awon gaba da shi da wasu mazauna yankin.

Wasu mutum biyu sun samu raunuka yayin harin, yayin da wani daga cikin ’yan bindigar ya harbi ɗan uwansa bisa kuskure, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Har yanzu, rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ba ta fitar da wata sanarwa kan sakin tsohon shugaban NYSC ɗin ba.

Satar mutane da hare-haren ‘yan bindiga na ci gaba da zama babbar barazana ga tsaro a Jihar Katsina da sauran sassan Najeriya.

Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro na fuskantar matsin lamba wajen shawo kan wannan matsala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Iran Tana Fuskantar  Makiya Na Waje Kafirar Da Munafikai
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  • Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Iran Da Haddiyar Daular Larabawa Sun Gudanar Da Taron Kwamitin Siyasa Da Al-adu Na Kasashen Biyu
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • Hukuma ta kama ciyaman kan zargin badaƙalar filin N100m a Kano
  • Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
  • Wata Mujalla Ta Zabi Shugaban NPA A Matsayin Gwarzonta Na Shekarar 2025
  • NAHCON Ta Naɗa Sabon Sakatare