Mataimakin wakilin kasar Sin a MDD Geng Shuang ya ce, ya kamata kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta karfafa hadin gwiwa da kasar Sudan, inda kuma ya bukaci gamayyar kasa da kasa da ta kara taka rawar gani wajen sasanta rikici a kasar.

Geng Shuang ya bayyana haka ne jiya, yayin wani taro da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kira don tantance rahoton da kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta gabatar dangane da batun Darfur na kasar Sudan.

A cewar Geng, yayin da kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ke gudanar da bincike a kasar Sudan, ya kamata ta yi mu’ammala sosai da gwamnatin kasar Sudan, kafin daukar wani mataki, ta yadda za a tabbatar da daidaita matsalar kasar, da magance tsanantar rikicin da ake samu. Kana ya kamata a aiwatar da dokokin kasa da kasa cikin daidaito, ba tare da siyasantar da harkokin shari’a, da bambanta ma’auni bisa wurin da ake ciki ba. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sudan

এছাড়াও পড়ুন:

Jama’ar Duniya Sun Soki Matakin Amurka Na Matsawa Kasashe Ta Hanyar Kakaba Haraji 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • Sakon Sakatare Janar Na Majalisar Dinkin Duniya Na Murna Fara Azumin Ramadan
  • Fitaccen Fim Din Na Kasar Sin Mai Suna “Ne Zha 2” Ya Zama Na 7 A Jerin Fina-finai Mafi Samun Kudi A Duniya
  • Rasha Za Ta Bunkasa Kai Wa  Nahiyar Afirka Alkama
  • Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
  • Kasashen Afrika Ta Kudu, Malasiya Da Colombia Zasu Hana Jiragen Ruwa Dauke Da Makamai Tsayawa A Tashoshin Jiragen Ruwansu
  • Jama’ar Duniya Sun Soki Matakin Amurka Na Matsawa Kasashe Ta Hanyar Kakaba Haraji 
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu