Babban rukunin gidajen rediyo da telabijin na kasar Sin (CMG) ya yi wani nuni na musamman na fitilu a jikin wasu manyan gine-gine guda 2 na kasar Afirka ta Kudu da na kasar hadaddiyar daular Larabawa ta UAE.

Nunin fitilun da aka yi a jikin ginin “The Leonardo”, gini mafi tsayi a kasar Afirka ta Kudu dake birnin Johannesburg, ya kunshi alamun shagalin murnar bikin bazara na kasar Sin da CMG din ya tsara, da zane-zanen salon musamman na murnar bikin bazara na Sin, wadanda suka burge jama’ar birnin Johannesburg sosai.

A sa’i daya kuma, nunin fitilun na CMG shi ma ya hau bangon hasumiyar Burj Khalifa dake Dubai na kasar UAE, wadda ta kasance gini mafi tsayi a duniya. (Bello Wang)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah

Sarkin Kano mai daraja ta daya wanda ya bayyana zaman lafiya a matsayin kashin bayan ci gaban kowace al’umma, don haka, ya amince da janye duk wasu shirye-shiryen bikin hawan Sallah mai ban sha’awa, wanda ofishin majalisar dinkin duniya mai kula da al’adu (UNESCO) ta bayyana a matsayin gadon bil’adama mara misaltuwa.

 

LEADERSHIP ta rawaito cewa, kwamishinan ‘yansandan jihar, CP Adamu Bakori ne ya sanar da dakatar da bikin hawan Sallah, saboda barazanar tsaro da jami’an leken asiri suka rahoto a jihar.

 

Dangane da haka, Sarki Sanusi ya yi kira ga al’umma da su kasance masu zaman lafiya da bin doka da oda tare da bayar da hadin kai ga jami’an tsaro domin tabbatar da doka da oda a lokutan bukukuwan Sallah da kuma bayan bikin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • HKI Ta Sake Kai Wa Unguwar Dhajiya Dake Beirut Hari
  • Ana Share Fagen Gudanar Bikin Baje Kolin Kayayyakin Da Ake Shigar Da Su Kasar Sin Yadda Ya Kamata
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin
  • Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya