Bugu da ƙari, dokar za ta bai wa direbobin da ke jigilar fasinjoji damar kula da yanayin fasinjojin da za su ɗauka ta yadda in sun ga yara dole sai sun tantance wanene ya ɗaukosu kuma meye nasabarsu dukka da nufin daƙile satar yara da safararsu.

 

Sannan gwamnan ya kuma sanya hannu kan dokar da ta bai wa kamfanonin sadarwa (Telecom Service Providers) dama ta yadda ba za a cajesu ko kwabo ba, da nufin inganta lamarin yanar gizo da inganta kamfanonin sadarwa domin jama’a suke morar amfani da tauraruwar ɗan adam da nufin sauƙaƙa harkokin kasuwanci a jihar.

 

Gwamnan ya yi gargaɗin cewa duk wani direban da ya ƙi bin umarnin da aka sanya na sanya ido kan yaran da ake safararsu doka za ta hau kansa. Sannan, ya ce ba za su lamunci yadda ake sace yaran jihar ana kaisu kudu.

 

Ya bayar da misalin baya-bayan da aka ceto wasu yaran jihar su uku daga jihar Anambra bayan da wata mata ta sace su a wani gidan haya. Don haka ne ya nemi Sarakuna da masu unguwanni da su ƙara bada tasu gudunmawar domin cimma nasarar kare yara ƙanana a jihar.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da Muƙaddashin Shugaban Ma’aikata kuma babban Sakatare na sashin shirye-shirye, Salisu Mustapha, bisa zargin yin kutse a albashin ma’aikatan gwamnati da rashin biyan wasu daga cikinsu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar daren Alhamis, an bayyana cewa dakatarwar ta fara aiki nan take, tare da umartar Mustapha da ya sauka daga matsayin babban Sakatare don bai wa kwamitin bincike damar gudanar da aikinsa ba tare da katsalandan ba.

Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Zaftare Albashin Ma’aikata

A don ci gaba da gudanar da harkokin ofishin, gwamnan ya nada Malam Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na bincike, kimantawa da tsare-tsare (REPA), a matsayin sabon muƙaddashin shugaban ma’aikata har sai an kammala bincike.

Wannan matakin na zuwa ne bayan kafa kwamitin mutum bakwai ƙarƙashin Hon. Abdulkadir Abdussalam da ke da wa’adin kwanaki bakwai don gano gaskiyar lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
  • Hamas Ta Bukaci Falasdinawa A Birnin Qudus Su Sabawa Dokar Takaita Yawan Masu Shiga Masallacin Al-Aksa A Kudus
  • A Yau Ce Dokar Haramta Amfani Da Tankunan Mai Masu Daukar Lita 60,000 A Najeriya
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗin 2025 na N54.99trn
  • Tinubu ya sanya hannu a kasafin kuɗi na N54.99trn
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
  • Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano