Gwamnan Bauchi Ya Rantsar Da Mashawarta 11, Ya Horesu Kan Aiki Tuƙuru
Published: 29th, January 2025 GMT
Sabbin waɗanda aka rantsar sun haɗa da Hon. Sanusi Khalifa, babban mashawarci kan albarkatun ƙasa; Hon. Haladu Ayuba, Mai Bada shawara kan daidaita ɗabi’un jama’a; Hon. Jidauna Tula, babban shawarcesa kan harkokin Shari’a da kuma Hon. Adamu Bello da aka sanya a matsayin babban mashawarci a ɓangaren kasuwanci da masana’antu.
Sauran sun haɗa da Alh. Danladi Mohammed Danbaba, babban mai bada shawara kan harkokin jin-ƙai; Hon. Sani Mohammed Burra, babban mai bada shawara kan harkokin majalisar dokokin jihar da na tarayya; Hon. Yakub Ibrahim Hamza, babban mai bada shawara kan ilimi mai zurfi da kuma Hon. Shitu Zaki da ya zama babban mai bada shawara kan harkokin siyasa.
Ƙarashin su ne Usman DanTuraki, babban mai bada shawara kan kan harkokin kungiyoyin kwadago; Farfesa Simon Madugu Yalams, mashawarci kan harkokin fasaha da koyar da sana’o’i sai kuma Abubakar Abdulhamid Bununu, mai bada shawara kan haɗin kai jama’a da yankuna.
Yayin da yake taya waɗanda ya nada murna, gwamna Bala Muhammad ya horesu da su nuna kwazo da kamala, dattako da sanin ya kamata yayin da suke hidimtawa jama’an jihar.
Ya nuna kwarin guiwarsa a kansu da cewa tabbas yana da yaƙinin gudunmawarsu zai taimaka sosai wajen cimma nasarori da manufofin gwamnatin jihar.
কীওয়ার্ড: kan harkokin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade a Ƙaramar Hukumar Arewa, Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum shida a makon da ya gabata.
Maharan sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, sannan suka hallaka ɗaya a Bagiza yayin harin da suka kai domin satar shanu.
Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren DankaliWannan ta’addanci ya jefa mazauna yankin cikin tsananin fargaba.
Gwamna Nasir Idris ya bayar da tabbacin inganta a tsaro jihar.
Ganin yadda mutane ke cikin tsoro, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kai ziyarar jaje ƙauyukan a ranar Asabar.
Ya tabbatarwa da al’ummar yankin cewa gwamnati na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar tsaro, musamman a yankin Kebbi ta Kudu.
Gwamnan ya bayyana cewa mafi yawan hare-haren da ake fuskanta a Kebbi na zuwa ne daga maƙwabtan jihohi.
“Tun daga lokacin da muka hau mulki, muna ɗaukar matakan da suka dace domin magance matsalar tsaro, kuma muna samun ci gaba.
“Rashin ɗaukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro a wasu maƙwabtan jihohi yana bai wa ’yan bindiga damar kutsowa cikin yankunanmu suna kai hari,” in ji Gwamnan.
Ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
A yayin ziyarar, Gwamna Nasir Idris ya bayar da tallafin miliyan 10 ga iyalan waɗanda aka kashe.
Haka kuma, ya bayar da umarnin gina Masallacin Juma’a da kuma bohol guda biyu da ke amfani da hasken rana a ƙauyen Rausa Kade.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Hon. Sani Aliyu Tela, ya jinjina wa Gwamnan bisa wannan kulawa.
Ya bayyana cewa harin ya faru ne a daren Alhamis, inda ’yan bindiga suka kai farmaki domin satar dabbobi.
“Sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, suka harbi mutum ɗaya a Bagiza. Mun yaba da kulawar da kake ba mu,” in ji shi.
Jama’a dai na fatan matakan da gwamnati ke ɗauka za su kawo ƙarshen hare-haren da suka addabi yankin.