Aminiya:
2025-04-25@02:11:34 GMT

DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Published: 29th, January 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Son haihuwar ’ya’ya maza fiye da ‘ya’ya mata abu ne da ake samu tun tale-tale a tsakanin al’ummomi daban-daban.

A tsakanin wasu al’ummomin, samun da namiji abin alfahari ne wanda kuma yake nuni da cigaba da dorewar ahali; sai dai ba a cika bai wa haihuwar ‘ya mace irin wannan muhimmancin ba.

Ko waɗanne dalilai ne suka sa wasu mutane suka fi son samun ’ya’ya maza a kan ’ya’ya mata?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Noma Don Samun Kuɗaɗen Shiga DAGA LARABA: Me Ya sa Matasa Ba sa Ɗaukar Koyarwa A Matsayin Sana’a?

Shirin Daga Laraba na wannan mako zai yi duba ne a kan dalilan da suka sa mutane suka fi son haihuwar ’ya’ya maza a kan ’ya’ya mata.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haihuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen AES sun kafa gidan rediyo don yaƙar farfagandar turawa

Ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, ƙarƙashin inuwar Ƙungiyar Ƙasashen Sahel (AES), sun sanar da shirinsu na ƙaddamar da gidan rediyo na haɗin gwiwa.

Ƙasashen guda uku, waɗanda duk a halin yanzu suke ƙarƙashin mulkin soja, sun jaddada cewa sun kafa gidan rediyon ne da nufin daƙile farfagandar ƙasashen waje da kuma isar da “ingantattun bayanai na gaskiya” ga ’yan ƙasarsu.

Sanarwar tasu ta kasance bayan ƙaddamar da gidan talabijin ɗinsu na intanet na haɗin gwiwa da suka yi a watan Disamba na 2024, wanda suka bayyana a matsayin dandamali da aka samar domin “yaƙi da yaɗa labaran ƙarya.”

Baya ga waɗannan ayyukan watsa labarai, a baya ƙungiyar ta nuna sha’awarta ta kafa kamfanin jiragen sama na yankin da kuma bankin saka hannun jari, wanda ya ƙara nuna jajircewarsu ga haɓaka haɗin kai da ci-gaba a tsakanin ƙasashe mambobin AES.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya

A watan Janairu na 2025 ne  ƙasashen uku da suka kafa ƙungiyar ta AES, suka sanar da ficewarsu a hukumance daga Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS).

Makonni uku da suka gabata, ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkin sojoji, sun ɗora harajin shigo da kaya na kashi 0.5 bisa ɗari a kan kayayyaki daga ƙasashen ECOWAS.

Harajin ya shafi duk kayayyakin da suka shigo daga ƙasashen ECOWAS zuwa kowace daga cikin ƙasashen uku, banda kayan agajin jin kai.

Wannan tsarin ya yi karo da shirin ECOWAS na tabbatar da zirga-zirgar kayayyaki a tsakanin mambobinta da ƙasashen AES duk da ficewarsu a hukumance daga ƙungiyar a watan Janairu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Ministan Tsaron Pakistan Ya Yi Wa Pakistan Barazanar Kai Mata Hari Mai  Tsanani
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • Ƙasashen AES sun kafa gidan rediyo don yaƙar farfagandar turawa
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 113
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Sin: Amurka Ta Buga Harajin Fito Kan Sassa Daban Daban Ba Tare Da Nuna Sanin Ya Kamata Ba
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya