Aminiya:
2025-03-02@20:21:51 GMT

DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Published: 29th, January 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Son haihuwar ’ya’ya maza fiye da ‘ya’ya mata abu ne da ake samu tun tale-tale a tsakanin al’ummomi daban-daban.

A tsakanin wasu al’ummomin, samun da namiji abin alfahari ne wanda kuma yake nuni da cigaba da dorewar ahali; sai dai ba a cika bai wa haihuwar ‘ya mace irin wannan muhimmancin ba.

Ko waɗanne dalilai ne suka sa wasu mutane suka fi son samun ’ya’ya maza a kan ’ya’ya mata?

NAJERIYA A YAU: Dabarun Noma Don Samun Kuɗaɗen Shiga DAGA LARABA: Me Ya sa Matasa Ba sa Ɗaukar Koyarwa A Matsayin Sana’a?

Shirin Daga Laraba na wannan mako zai yi duba ne a kan dalilan da suka sa mutane suka fi son haihuwar ’ya’ya maza a kan ’ya’ya mata.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Haihuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Za Mu Doke Atletico Madrid Har Gida, Hansi Flick

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona, Hansi Flick, ya bayyana cewa kungiyarsa za ta je har gidan Atletico Madrid ta doke ta a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin Coppa Del Rey, bayan da Barcelona da Atletico Madrid suka tashi 4-4 a wasan farko zagayen daf da karshe a Copa del Rey ranar Talata a filin wasa na Estadi Olimpic Lluis Companys.

Minti daya da fara wasan Atletico Madrid ta fara cin kwallo ta hannun Julian Albarez, sannan Griezmann ya kara ta biyu a minti na biyar Tsakani amma daga baya Barcelona ta zare daya ta hannun Pedri a minti na 19, sannan Cubarsi ya farke ta biyu minti uku Tsakani sannan kafin hutu Barcelona ta kara ta uku ta hannun Martinez, haka suka je zagayen farko Barcelona na cin 3-2.

Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne, sai Barcelona ta ci ta hudu a karawar ta hannun Lewandowski kai kace an tashi da Atletico Madrid a wasan amma daga baya kungiyar da Diego Simeone ke jan ragama ta zare kwallo ta uku ta hannun Llorente daga baya ta zare ta hudu ta hannun Sørloth dab da za a tashi daga wasan wanda yaja hankalin ‘yan kallo a duniya.

Wannan shi ne karo na biyu da suka kece raini a tsakaninsu a bana, bayan da Atletico ta je ta doke Barcelona a La Liga ranar 21 ga watan Disamba kuma a ranar Laraba 4 ga watan Afirilu, Atletico za ta karbi bakuncin wasa na biyu a daf da karshe a Copa del Rey. Barcelona ce ta daya a kan teburin La Liga da maki 54, iri daya da na Real Madrid ta biyu da kuma Atletico mai maki 53 ta ukun teburin babbar gasar tamaula ta Sifaniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa
  • Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha 
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Za Mu Doke Atletico Madrid Har Gida, Hansi Flick
  • Abubuwan Sha Domin Karin Ni’ima Ga Mata
  • Haleyen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (1)
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa
  • Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata