Aminiya:
2025-03-03@09:22:59 GMT

Kiristoci sun yi addu’ar ɗorewar zaman lafiya a Kudancin Kaduna

Published: 29th, January 2025 GMT

Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci na Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi kira ga al’ummar yankin da su rungumi haɗin kai da ƙaunar juna a matsayin tubalin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.

Shugaban ƙungiyar SKCLA, Fasto Emmanuel Nuhu Kure ne ya yi wannan kiran ga mazauna yankin a wajen taron addu’ar shekara-shekara da ake gudanarwa a garin Kafanchan don kyautata alaƙarsu da Ubangiji tare neman ɗauki daga gare Shi don samun zaman lafiya da wadata.

DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura

“Lokaci ya yi da za mu haɗa kai da tunanin mu waje ɗaya da manufa ɗaya don sake gina al’ummomin Kudancin Kaduna,” inji Kure.

“Dole ne mu koyi son makwabtanmu musulmai ba tare da wariya ba. Idan har babu haɗin kai, ba za mu samu makoma mai kyau ba.”

Malamin ya jaddada buƙatar sake gina yankin inda ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da ta jiha kan inganta tsaro a yankin.

“A cikin shekaru biyu da suka gabata zamu iya cewa mun samu zaman lafiya, yanzu za mu iya numfasawa da kyau kuma mu yi barci idanunmu biyu a rufe, muna jin daɗin zaman lafiyar da ke gudana,” inji shi.

Kure ya kuma yi kira ga manyan mutane daga Kudancin Kaduna da su yi amfani da wannan damar na zaman lafiya wajen kafa masana’antu da za su samar da aikin yi ga matasan yankin ba tare da jiran gwamnati sai ta yi komai ba.

Babban baƙo mai jawabi, Bishop Zakka Nyam na Cocin Anglikan da ke Kano, ya bayyana fatansa na kasancewar shekara 2025 da ta zamo shekarar sauyi ga Kudancin Kaduna.

Ya ce lokaci ya yi da jama’ar yankin za su yi watsi da dabi’ar yawaita gine-ginen Otal a yankin maimakon haka su fara gina masana’antu don sarrafa abubuwan da ake nomawa a yankin.

A nasa jawabin, Mataimakin Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Kaduna, Hon. Henry Magaji Danjuma ya bayyana yankin Kudancin Kaduna a matsayin yanki mai yalwar albarkatu, tare da yin kira ga mazauna yankin da su mara wa gwamnatinsu baya don samun ƙarin romon dimokuraɗiyya.

An gudanar da addu’o’i da waƙe-waƙen ibada musamman don ceto yankin, da Jihar Kaduna da kuma ƙasar baki ɗaya.

Taron addu’o’in da aka gudanar a Kudancin Kaduna

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran

Rundunar Basij a yankin kudu maso gabacin kasar Iran ta bada sanarwan shahadar dakarunta guda biyu a jiya Asabar.

Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar Iran, ya nakalto rundunar IRGC na yankin ya na bada sanarwan shahadar Hojjatoleslam Sadeq Mahmoudi da kuma Milad Damankesh a lokacinda suke komawa gida daga wurin aiki a cikin wata mota tasu.

Labarin ya kara da cewa shahidan biyu sun hadu da ajalinsu ne a lokacinda wasu yan ta’adda suka bude wuta a kan motarsu a lokacinda suke wucewa a wata unguwa zuwa gidajensu.

Lardin Sitan Baluchistan wanda ke kan iyaka da kasar Pakistan dai ya dade yana fada da kungiyoyin yan ta’adda wadanda suke shigowa kasar daga kasar Pakistan, wadanda kuma suke samun taimako kasashe waje, musamman kasashen yamma da wasu kasashe makobta.

Wata kungiya wacce ake kira ‘Jashul Adle” ce ta saba daukar nauyin kashe mutane a yankin, fararen hula da sojoji wadanda suke taimakawa don tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
  • Lavrov Ya Yi Watsi Da Batun Aike Wa Da Dakarun Zaman Lafiya A Kasar Ukiraniya
  • Kasancewar Zaman Lafiya Na Dogon Lokaci Tsakanin Sin Da Amurka Abu Ne Da Ya Zama Wajibi
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Motocin Buldoza Suna Ta Rusa Gidajen Falasdinawa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria
  • An Yi Jana’izar Shahidan Hizbullah Fiye Da 100 A Kudancin Lebanon
  • Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a
  • Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana