Masu Zanga-zanga Sun Farmawa Ofisoshin Jakadancin Amurka Da Na Faransa A DR Congo
Published: 29th, January 2025 GMT
Masu zanga-zanga sun kai hari kan ofisoshin jakadancin kasashen waje da dama hari a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo (DRC).
An bayar da rahoton cewa, fusatattun masu zanga-zangar sun kai wa ofisoshin jakadancin Amurka, Faransa, Belgium, Rwanda, Uganda, Kenya da Afirka ta Kudu hari.
Masu zanga-zangar dai na neman hadin kan kasashen waje da yunkurin kasa da kasa na shiga tsakani na soji da kuma dakatar da ‘yan tawayen M23 da ke ci gaba da mamaye wasu sassan yankin gabashi.
‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa amma masu zanga-zangar sun samu damar shiga sassan harabar, inda suka yi banka wuta.
Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana yi da kungiyar ta M23 ya yi Kamari a baya bayan nan, inda suka kwace iko da Goma babban birnin gabashin Congo, ko da yake rundunar sojin Congon ta ce har yanzu tana iko da kashi 80 na birnin.
Masu zanga-zangar a Kinshasa sun bukaci kasashen duniya su matsa lamba kan kasar Rwanda kan ci gaban da dakarun ‘yan tawayen suka yi.
Tashin hankali a yankin da ake fama da rikicin kabilanci ya haifar da daya daga cikin manyan matsalolin jin kai a duniya.
A shekara ta 2012, ‘yan tawayen M23 sun mamaye birnin na Goma na wani dan lokaci kafin a tilasta musu janye dakarunsu a karkashin matsin lamba daga kasashen duniya.
A shekara ta 2021, dakarun ‘yan tawayen sun sake haduwa bisa tallafin da suke samu daga kasar Rwanda, a cewar gwamnatin Kinshasa da kwararrun MDD, saidai gwamnatin Kigali na mai musanta hakan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Masu zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Wajibi Ne Kasashen Musulmi Su Kara Karfafa Alakokinsu
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce inganta hadin kai da alaka tsakanin kasashen musulmi da suka hada da Iran da Malaysia na daga cikin abubuwan da ake bukata a halin da ake ciki a duniya.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da ministan harkokin wajen Malaysia Dato’ Seri Utama Haji Mohamad Bin Haji Hasan a birnin Tehran a wata ziyara da ya kai kasar Iran.
Ya ce a halin yanzu gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana aiwatar da abin da take yin a laifuka da wuce gona da iri a yankin saboda kan musuylmi ba hade yake ba.
Ya kara da cewa samar da hadin kai tsakanin jami’ai da ‘yan siyasar kasashen musulmi zai taka muhimmiyar rawa wajen kawar da bambance-bambance, rashin fahimta da talauci a cikin kasashen musulmi.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take domin kara fadada hanyoyin sadarwa da kasashen musulmi ciki har da Malaysia a dukkan fannoni in ji shugaban na Iran.
A ci gaba da jawabin nasa, Pezeshkian ya yi nuni da cewa, an gudanar da taron kwamitin hadin gwiwa na kasashen Iran da Malaysia karo na 8 a birnin Tehran a safiyar Laraba bayan shafe shekaru 17 ana yin irin wannan taro.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Malaysia ya ce alakar da ke tsakanin Tehran da Kuala Lumpur ta ginu ne bisa fahimta da ‘yan uwantaka.
Ya bayyana aniyar Malaysia na bunkasa alaka da Iran da kuma amfana da karfin Jamhuriyar Musulunci ta fuskar kimiyya, fasaha, ilimi, kayan abinci da noma.