HausaTv:
2025-04-02@15:45:16 GMT

Masu Zanga-zanga Sun Farmawa Ofisoshin Jakadancin Amurka Da Na Faransa A DR Congo

Published: 29th, January 2025 GMT

Masu zanga-zanga sun kai hari kan ofisoshin jakadancin kasashen waje da dama hari a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo (DRC).

An bayar da rahoton cewa, fusatattun masu zanga-zangar sun kai wa ofisoshin jakadancin Amurka, Faransa, Belgium, Rwanda, Uganda, Kenya da Afirka ta Kudu hari.

Masu zanga-zangar dai na neman hadin kan kasashen waje da yunkurin kasa da kasa na shiga tsakani na soji da kuma dakatar da ‘yan tawayen M23 da ke ci gaba da mamaye wasu sassan yankin gabashi.

‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa amma masu zanga-zangar sun samu damar shiga sassan harabar, inda suka yi banka wuta.

Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana yi da kungiyar ta M23 ya yi Kamari a baya bayan nan, inda suka kwace iko da Goma babban birnin gabashin Congo, ko da yake rundunar sojin Congon ta ce har yanzu tana iko da kashi 80 na birnin.

Masu zanga-zangar a Kinshasa sun bukaci kasashen duniya su matsa lamba kan kasar Rwanda kan ci gaban da dakarun ‘yan tawayen suka yi.

Tashin hankali a yankin da ake fama da rikicin kabilanci ya haifar da daya daga cikin manyan matsalolin jin kai a duniya.

A shekara ta 2012, ‘yan tawayen M23 sun mamaye birnin na Goma na wani dan lokaci kafin a tilasta musu janye dakarunsu a karkashin matsin lamba daga kasashen duniya.

A shekara ta 2021, dakarun ‘yan tawayen sun sake haduwa bisa tallafin da suke samu daga kasar Rwanda, a cewar gwamnatin Kinshasa da kwararrun MDD, saidai gwamnatin Kigali na mai musanta hakan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Masu zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Tafi Faransa Ziyarar Aiki Na Mako 2

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bar Abuja a yau Laraba zuwa Paris, na ƙasar Faransa, domin ziyarar aiki ta makonni biyu.

A cewar mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu zai yi bitar mulkinsa na rabin wa’adi, inda zai tantance nasarorin da ya cimma da kuma irin sauye-sauyen da yake aiwatarwa.

Haaland Zai Ziyarci Likita Saboda Raunin Da Ya Samu A Ƙafa

Sanarwar ta ce wannan lokaci zai ba shi damar tsara hanyoyin da za su inganta ci gaban ƙasa yayin da yake shirin cika shekaru biyu a kan mulki.

Duk da kasancewarsa a waje, Onanuga ya tabbatar da cewa Shugaba Tinubu zai ci gaba da gudanar da harkokin gwamnati tare da tuntuɓar manyan jami’ansa har zuwa lokacin da zai dawo gida.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Tafi Faransa Ziyarar Aiki Na Mako 2
  • Tinubu zai tafi ziyarar makonni biyu a Faransa
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin