Hadakar Kasashen Sahel Sun Yi Ban Kwana Da Kungiyar ECOWAS
Published: 29th, January 2025 GMT
Hadakar Kasashen Sahel na AES, sun yi ban kwana da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS ko CEDEAO a hukumance bayan shekaru 50 na kasancewa mamba a cikinta.
Ya zuwa wannan Laraba, 29 ga Janairu, bangarorin biyu sun raba gari duk da cwa kungiyar ta ECOWAS ta baiwa kasashen wa’adin watannin shida ko zasu canza ra’ayi.
Kasashen na Mali, Nijar da kuma Burkina Faso sun ce bakin alkalami ya riga fa ya bushe.
A jiya Talata al’umomin kasashen guda uku sun gudanar da gangami da jerin gwano na nuna murnar ficewa daga kungiyar da suka ce ta zama ‘yar amshin shatan kasashen yamma musamman faransa wacce ta yi musu mulkin mallaka.
Haka zalika a wannan Larabar ce kasashen uku zasu kaddamar da fasfonsu, amma sun ce masu rike da fasfon Ecowas zasu ci gaba da amfani da shi, kuma sauren al’umomin kasashen ECOWAS zasu ci gaba da shige da fice cikin ‘yanci.
Matakin Kasashen na AES bai shafi kungiyar UEMOA ta kasashe guda 8 da ke anfani da kudin bai daya na sefa ba, Don haka ‘yancin zirga-zirgar jama’a da kayayyaki ya kasance tabbatacce a wannan yanki wanda ya hada kasashen Ivory Coast, Senegal da Benin.
A ranar 28 ga watan Janairu 2024, kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar suka ba da sanarwar ficewa daga kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka. Hakan ya biyo bayan kirkirar kungiyar AES na Kawancen Sahel a ranar 6 ga watan Yulin 2024.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
Shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa kasar Yemen a shirye take ta sake shiga yaki idan yarjeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu ta wargaje.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sayyid Huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar ta hotunan bidiyo a jiya 28 ga watan Fabrairun shekara ta 2025.
Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya bayyana cewa birnin Tel’aviv wato Yafa, zai zama babban wurin da makaman kungiyar zasu nufi idan hakan ya faru.
Huthi ya ce “Idan yaki ya sake barkewa za mu kai hare-hare a ko ina a HKI sannan birnin Tel’aviv zai za ma babbar manufar makamammu.
Yace: Kasar Yemen ta na kallom yadda al-amura suke tafiya a ayyukan tsagaita wutar, kuma ta na kallon yadda HKI take sabawa wasu abubuwan da ke cikin yarjeniyar. Ya kuma ambaci yadda HKI ta ki janyewa daga rafah da kuma yankin philidelfiya na kan iyaka da kasar Masar. Wanda kuma ya sabawa yarjeniyar. Sannan ya kammala da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na kodaitar da HKI da yin hakan.