HausaTv:
2025-04-29@23:05:04 GMT

Jagora : Gaza Ta Durkusar Da Gwamnatin Isra’ila Dake Samun Goyan Bayan Amurka

Published: 29th, January 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce karamin yankin Gaza ya durkusar da gwamnatin Isra’ila duk da makaman da ta ke dasu da kuma cikakken goyon bayan Amurka.

Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa : tsayin daka da aka fara a Iran din, ya jawo farkawar wasu al’ummar musulmi kuma durkusar da Isra’ila a Gaza da Labanon misali ne.

Jagoran ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin wata ganawa da jakadun kasashen musulmi a birnin Teheran, a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan zagayowar ranar aiko da sakon annabta ga Manzon Allah Muhammad (SAW).

Jagoran ya ce “A yau, bayanin da muke bayarwa na mulkin mallaka da girman kai yana bayyana gaba daya daga gwamnatin Amurka.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin dubban Falasdinawan Gaza suka fara komawa yankin bayan cimma yarejejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila.

Ofishin yada labarai na gwamnati a zirin Gaza ya sanar da cewa Falasdinawa kusan 350,000 da suka rasa matsugunansu ne suka koma gida a gabar tekun a ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar.

“Wannan ya zo ne bayan kwanaki 470 na kisan kiyashi da sojojin mamaya na Isra’ila suka yi,” wanda ya yi sanadin shahadar Falasdinawa sama da 47,000 tare da wargaza yankin.

An bayyana cewa sama da kashi 90%, na yankin ya lalace sakamakon hare haren Isra’ila wandanda suka ruguza duk wasu wurare da cibiyoyi masu matukar mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, makarantu, gidajen jama’a wuraren samar da ruwan sha da wutar lantarki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike

Rahotonni sun tabbatar da cewa: Da tsakar daren jiya Litinin wayewar garin yau Talata, sojojin mamayar Isra’ila dauke da motocin soji guda hudu da wasu sojoji masu tafiyar kafa sun kutsa cikin yankunan kasar Siriya daga titin Al-Hurriya, inda suka wuce titin Al-Kassarat, zuwa Talat Jabata Al-Khashab.

Majiyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Siriya ta bayyana cewa: Sojojin mayar sun kafa shingen binciken ababen hawa inda suka tsaya suna binciken ababan hawa da ke wucewa, sannan suka haska wuta don gano hanyar kafin su fita ta hanyar da suka shiga. Jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma suna shawagi a sararin samaniyar birnin Damascus fadar mulkin kasar ta Siriya.

A jiya Litinin ma, sojojin mamayar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wasu sansanoni na rundunar sojin ta 36 ta musamman da aka fi sani da Ain al-Burj a gabashin kauyen Qala’at Jandal da ke cikin karkarar birnin Damascus, tare da kafa wani sansanin soji a saman dutsen Barbar domin sa ido kan motsin da ake yi a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa
  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham
  • Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba
  • Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas