Leadership News Hausa:
2025-04-22@18:00:12 GMT

Ademola Lookman Ba Zai Buga Wasan Atalanta Da Barcelona Ba

Published: 29th, January 2025 GMT

Ademola Lookman Ba Zai Buga Wasan Atalanta Da Barcelona Ba

Ɗan wasan Nijeriya kuma gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar Afrika, Ademola Lookman, ba zai buga wasan da Atalanta za ta kara da Barcelona a gasar cin kofin Zakarun Turai yau Laraba ba, sakamakon rauni da ya ji a gwiwarsa.

A wata sanarwa da kulob ɗin Atalanta ya fitar, ya ce ɗan wasan mai shekaru 27 ya samu rauni a gwiwar dama a lokacin atisayen safiyar Talata, wanda ya hana shi tafiya Spain don buga wasan da ƙungiyarsa ke neman cancantar shiga zagayen 16 na ƙarshe.

Tinubu Ya Yi Alƙawarin Inganta Wutar Lantarki A Nijeriya Gwamnan Bauchi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Da Za Ta Daƙile Satar Yara A Bauchi 

Duk da cewa kulob ɗin bai bayyana tsawon lokacin da Lookman zai yi jinya ba, kafofin labarai a Italiya sun ruwaito cewa zai ɗauki kusan wata guda kafin ya dawo.

Lookman dai babban rashi ne ga Atalanta, duba da cewa ya zura ƙwallaye 14 tare da bayar da taimako a ƙwallaye shida a wannan kakar wasa.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barcelona Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa babu wani kamfen batanci da zai hana Gwamna Dauda Lawal aiwatar da ayyukan da suka shafi al’umma a fadin jihar.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai da sadarwa na gwamna, Malam Salihu Nuhu Anka ya rabawa manema labarai a Gusau.

 

A cewar Anka, Gwamna Lawal ya fara aiki ne a wani aikin ceto, kuma tuni mazauna jihar suka fara cin ribar dimokuradiyya.

 

Ya bayyana cewa hankalinsa ya karkata ne kan kalaman da ya bayyana a matsayin maras tushe da wani tsohon Kwamishinan Yada Labarai, Ibrahim Magaji Dosara ya yi, yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya kalubalanci kalaman da Gwamna Lawal ya yi a wata hira da ya yi da shi kwanan nan.

 

“A yayin taron manema labarai, Dosara ya kai wa Gwamna Dauda Lawal hari cikin rashin kunya a kokarinsa na burge tsohon Gwamna Bello Matawalle,” Anka ya yi zargin.

 

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Manufar Kasarsa Da Shirin Kare Muradunta A Duk Wata Yarjejeniya
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • Putin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da Iran
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
  • Burnley Da Leeds United Sun Dawo Gasar Firimiya Lig 
  • Shugaba Tinubu Zai Dawo Nijeriya A Yau Litinin Bayan Ziyarar Aiki A Turai
  • Babu Wata Suka Da Za Ta Hana Gwamna Dauda Lawal Aiwatar da Ayyuka.
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu