Aminiya:
2025-03-22@02:29:15 GMT

Mun kama mutum 46 da miyagun ƙwayoyi a Yobe — NDLEA

Published: 29th, January 2025 GMT

Hukumar yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi (NDLEA) reshen Jihar Yobe ta ce ta kama wasu haramtattun ƙwayoyi da nauyinsu ya kai kilo 537 tare da kama wasu mutum 46 da ake zargi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a shekarar 2024.

Kwamandan hukumar ta NDLEA a Jihar Yobe, Mista Abdulazeez Ogungboye ne ya bayyana hakan a Damaturu yayin da yake bitar ayyukan hukumar na shekara guda da ta gabata.

Kiristoci sun yi addu’ar ɗorewar zaman lafiya a Kudancin Kaduna DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Ya ce magungunan da aka kama sun haɗa da kilo 396.526 na tabar wiwi da kilo 141.2 na sauran kayayyakin maye.

Ogunboye ya ce hukumar ta miƙa mutane 21 cikin mutane 46 da ake zargi da aikata laifukan a gaban kuliya domin yanke musu hukuncin da ya dace da su, yayin da ake ci gaba da shari’ar 85 a Babbar Kotun Tarayya da ke Damaturu.

Kwamandan ya ce hukumar ta bayar da shawarwari ga mutane 219 da suka dogara da muggan kwayoyi tare da gudanar da gangamin wayar da kan jama’a a cikin al’umma, makarantu, ƙungiyoyin addini, da wuraren aiki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu

Rundunar ‘yan sandan Jihar Legas ta sanar da kama Mista Peter Dike da ake zargi da kashe matarsa ​​a gidansu da ke Unguwar Oke-Ira Ilogbo Eremi, Marogbo.

Rundunar ’yan sandan a ranar Alhamis ta bayyana cewa wanda ake zargin ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa har lahira a lokacin da suka yi ƙazamin faɗa da ya ɓarke a gidan nasu sanadin taƙaddama a ranar Laraba.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe Shahararren ɗan kasuwa Nasiru Ahali ya rasu a Kano

Wannan mummunan al’amari ya ƙara dagula al’amuran tashin hankali a cikin gidan ma’aratan da ya kawo sanadin mutuwar matar aure.

A watan Oktoban 2024, an kuma kama Motunrayo Olaniyi da laifin daɓa wa amaryarsa, Olajumoke wuƙa har lahira, a yayin wata hatsaniya mai zafi a gidan su a rukunin gidaje na Amazing Grace Estate, Elepe, a yankin Ikorodu.

Da yake ƙarin haske kan lamarin a ranar Laraba, jami’in hulɗa da jama’a na ’yan sandan, CSP Benjamin Hundeyin, ya bayyana cewa an sanar da jami’an tsaro na sashen Morogbo, kuma ba tare da ɓata lokaci ba suka isa wurin.

Hundeyin ya ci gaba da cewa, “An tabbatar da al’amarin, bayan da jami’an ‘yan sanda da ke sintiri a cikin garin da ke yankin suka samu labarin, sai suka shiga cikin gaggawa suka cafke wanda ake zargin, an samu wuƙar kicin guda ɗaya da tabo da jini daga wajensa, aka kawo shi ofishin aka yi masa tambayoyi.

“Ya amsa laifinsa, an ajiye gawar a ɗakin ajiyar gawa na babban asibitin Badagry, kuma za a miƙa ƙarar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Panti Yaba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic
  • Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu
  • Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul
  • An Bukaci Gwamnati A Kowani Mataki Da Ta Taimakawa Yaki Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
  • Da Ɗumi-ɗumi: Ana Fargabar Mutuwar Mutane Da Dama Yayin Da Tankar Mai Ta Fashe A Hanyar Zuwa Abuja 
  • Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe