Aminiya:
2025-02-17@16:28:41 GMT

Mun kama mutum 46 da miyagun ƙwayoyi a Yobe — NDLEA

Published: 29th, January 2025 GMT

Hukumar yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi (NDLEA) reshen Jihar Yobe ta ce ta kama wasu haramtattun ƙwayoyi da nauyinsu ya kai kilo 537 tare da kama wasu mutum 46 da ake zargi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a shekarar 2024.

Kwamandan hukumar ta NDLEA a Jihar Yobe, Mista Abdulazeez Ogungboye ne ya bayyana hakan a Damaturu yayin da yake bitar ayyukan hukumar na shekara guda da ta gabata.

Kiristoci sun yi addu’ar ɗorewar zaman lafiya a Kudancin Kaduna DAGA LARABA: Dalilan Da Mutane Suke Son Haihuwar Maza Fiye Da Mata

Ya ce magungunan da aka kama sun haɗa da kilo 396.526 na tabar wiwi da kilo 141.2 na sauran kayayyakin maye.

Ogunboye ya ce hukumar ta miƙa mutane 21 cikin mutane 46 da ake zargi da aikata laifukan a gaban kuliya domin yanke musu hukuncin da ya dace da su, yayin da ake ci gaba da shari’ar 85 a Babbar Kotun Tarayya da ke Damaturu.

Kwamandan ya ce hukumar ta bayar da shawarwari ga mutane 219 da suka dogara da muggan kwayoyi tare da gudanar da gangamin wayar da kan jama’a a cikin al’umma, makarantu, ƙungiyoyin addini, da wuraren aiki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone ofishin zaɓe INEC a Sakkwato

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ofishinta na Ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato ya ƙone ƙurmus, inda  gobarar ta lalata akwatunan zaɓe da sauran kayayyaki.

Mista Sam Olumekun, kwamishinan Hukumar INEC kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wata sanarwa.

Mutum 23 sun mutu da raunata wasu a haɗarin mota a gadar Kano Tinubu ya isa Ethiopia domin halartar taron AU

A cewarsa, a taron Hukumar INEC na mako-mako da aka saba gudanarwa a ranar Alhamis, hukumar ta lura da wani mummunan lamari na tashin gobara a ofishin ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato, kamar yadda sakatariyar gudanarwa mai kula da ofishin jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa ta ruwaito.

Ya ce gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Talata 11 ga watan Fabrairun 2025.

“Duk ginin ofishin ya lalace. Kayayyakin da suka lalace sun haɗa da tebura da kujeru da kayan aiki da kayan zaɓe da ake iya ɗauka, daga cikinsu akwai akwatunan zaɓe 558, rumfar kaɗa ƙuri’a 186, jakunkuna 186 na zaɓe da kuma kayayyakin da suka haɗa da manyan tankunan ruwa guda 12 (litta 1,000), tabarmin barci 400 da bokitan robobi 300.

“Rahoto na farko daga ofishinmu na jihar ya nuna cewa an samu ƙaruwar wutar lantarki kafin faruwar lamarin,” in ji Olumekun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau
  • Ƴansanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Ta Facebook A Kwara
  • Gwamnatin Yobe Ta Ɗauki Jami’an Kiwon Lafiya 42 Aiki
  • Mutum Biyu Sun Faɗa Komar ‘Yansanda Bisa Zargin Sata A Gombe
  • Boko Haram ta kashe kwamandoji da mayaƙan ISWAP 31 a Borno
  • Jiragen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa Sun Kashe Mutane 3 A Kudancin Kasar Lebanon
  • An Kama Ɗan Nijeriya Mazaunin Indiya Bisa Zargin Damfarar Kamfani Dala 13,361
  • Gobara ta ƙone ofishin INEC a Sakkwato
  • Mummunan Hatsari Ya Kashe Mutane 23, Da Yawa Sun Jikkata A Kano
  • Gobara ta ƙone ofishin zaɓe INEC a Sakkwato