Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da harin da aka kai kan fararen hula a Sudan

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai da kisan fararen hula a hare-haren da ake kai wa kan asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan tare da jaddada wajibcin mutunta ka’idoji da dokokin kare hakkin bil’adama a kasar.

Baqa’i” ya yi Allah wadai da kisan mutane a hare-haren da ake kai wa kan fararen hula da ababen more rayuwa, musamman asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya bayyana juyayinsa ga wadanda harin baya-bayan nan ya rutsa da su, musamman a birnin El Fasher fadar mulkin Darfur ta Arewa, inda ya jaddada bukatar kiyaye ka’idoji da na dokokin jin kai na kasa da kasa, musamman ka’idar haramta kai hare-hare kan wuraren fararen hula, tare da yin kira da a kawo karshen tashe-tashen hankula da samar da hanyoyin warware rikicin da ke faruwa a Sudan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a

Shadidan Hizbullah kimabi 130 ne aka yi jana’izarsu a yau jumma’a a kudancin kasar Lebanon. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran tanakalto kungiyar Hizbullah na fadar haka, ya kuma kara da cewa kungiyar ta gabatar da shihidar da dama saboda kare kasarsu, saboda kare kasar Lebanon daga mamayar HKI.

Labarin ya kara da cewa an gudanar da jana’izar ne a garuruwan Aitarun da kuma Aita shaab. Inda mutanen da dam dagayankin zuka halarta . Labarin ya kara da cewa Shahidan sun kai ga shahada ne a hare-haren da sojojin HKI suka kai kan kudancin kasar ta Lebanon a cikin watannin Octoba da kuma Nuwamba na shekara ta 2024.

Labarin ya kara da cewa a yakin dai mutanen leabin kimani 4000 ne suka rasa rayukansu mafi yawansu fararen hula ne wadanda basu san hawa ko sauka ba.

Kafin jana’izar yau ma, sojojin HKI da suke mamaye da wasu wurare a kudancin kasar Lebanon sun yi harbi da bindiga don tsoratar da mutane masu Jana’izar, wanda hakan ya kasance keta yarjeniyar da aka kulla da Ita

A dai dai lokacin ne sojojin HKI ta kashe manya-manyan shuwagabanni da kwamandojojin sojojin Hizbullah na kasar wanda ya hada har da shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah, da magajinsa Sayyid Hashin Safiyyuddiin, wadanda aka yi masu jana’iza a ranakin 23-24 na watan fabarairu da muke ciki a birnin Neirut babban birnin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Majalisar dokoki ta tsige ministan tattalin arziki saboda hauhawar farashi
  • Masar ta ki amincewa da duk wani yunkuri na kafa gwamnatin ‘yan adawa a Sudan
  • HKI Ta Yi Barazanar Shiga Rikicin Da Ya Barke  A Garin Jarmana Na Kasar Syria
  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Xi Ya Jaddada Ciyar Da Shirin Kasar Sin Mai Kwanciyar Hankali Zuwa Babban Mataki
  • Iran Ta Zama Zakara A Damben Gargajiya Ta 2025 UWW Wanda Aka Gudanar A Kasar Albaniya
  • An Yi Jana’izar Shahidan kungiyar Hizbullah Fiye Da 120 Kudancin Kasar Lebanon A Yau Jumma’a
  • Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
  • Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya
  • Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata