Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi Allah wadai da harin da aka kai kan fararen hula a Sudan

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai da kisan fararen hula a hare-haren da ake kai wa kan asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan tare da jaddada wajibcin mutunta ka’idoji da dokokin kare hakkin bil’adama a kasar.

Baqa’i” ya yi Allah wadai da kisan mutane a hare-haren da ake kai wa kan fararen hula da ababen more rayuwa, musamman asibitoci da cibiyoyin jama’a a Sudan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya bayyana juyayinsa ga wadanda harin baya-bayan nan ya rutsa da su, musamman a birnin El Fasher fadar mulkin Darfur ta Arewa, inda ya jaddada bukatar kiyaye ka’idoji da na dokokin jin kai na kasa da kasa, musamman ka’idar haramta kai hare-hare kan wuraren fararen hula, tare da yin kira da a kawo karshen tashe-tashen hankula da samar da hanyoyin warware rikicin da ke faruwa a Sudan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Zama Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Bakin Teku Karo Na 4 Asiya

Yan wasan kwallon kafa na kasar Iran sun zama zakara karo na 4 a kwallon kafa na yashin bakin teku a karo na 4 a cikin kasashen Asiya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ba bayyana a gasa ta karshe wanda kungiyar kwallon kafa ta yashin bakin take wanda aka gudanar tsakanin JMI da kuma Omman an tashi da ci 8-1.

Wannan nasarar dai ta tabbatar wa kasar Iran fifiko a wannan wasar har saw hudu a jere. Kuma ba’a taba samun nasara a kan ta gaba daya a dukkan wasannin da ta yi a duk tsawon gasar ba.

Mai horar da yan wasan Iran a wannan gasar Ali Nadiri ya bayyanawa IP kan cewa nasarar da JMI ta samu a wanna gabasa ya tabbatar da kokarinsu a wanna wasar, sannan da hadin kansu a wannan wasar wanda kuma hakan yake basu nasara a duk wasan da suka yi. Don haka muna alfakhari da sake maida wannan kofin gida Iran inji Nadiri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Iran: Larijani Ya Ce Iran Zata Fara Kera Makaman Nukliya Idan An Kai Mata Hari Kan Shirin Ta Na Makamashin Nuliya
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  • Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • Iran Ta Zama Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Bakin Teku Karo Na 4 Asiya
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen A Daren Jiya