Babban kwamishinan hukumar kula da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya “UNRWA” ya bayyana wa kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya cewa: Aiwatar da dokokin Isra’ila kan hukumar UNRWA zai zama bala’i

Babban Kwamishinan Hukumar Kula da ‘yan gudun hijiran Falasdinawa ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA), Philippe Lazzarini, ya ce: Aiwatar da cikakken dokar Majalisar Dokokin Haramtacciyar kasar Isra’ila ta Knesset kan hukumar UNRWA zai zama masifa, yana mai gargadin cewa: Rage ayyukan hukumar ta “UNRWA” a wajen tsarin siyasa, kuma a daidai lokacin da kwarin gwiwa daga kasashen duniya ya yi kadan, wanda hakan zai kawo cikas ga yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

Shafin watsa labaran Falasdinu na “Wafa” ya bayar da rahoton cewa: A jawabin da ya gabatar ga zaman kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya kan halin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya, gami da batun Falasdinu, a halin yanzu, Lazzarini ya jaddada cewa: Hukumarsa tana da matukar muhimmanci wajen tallafa wa al’ummar da suka shiga halin kaka-ni ka yi da kuma ci gaba da wanzar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta, amma duk da haka a cikin kwanaki biyu, ayyukan hukumar ya tsaya cak a yankunan Falasdinawa.

Ya yi gargadin cewa: Makomar miliyoyin Falasdinawa, da tsagaita bude wuta da kuma fatan samun mafita ta siyasa da za ta samar da dawwamammen zaman lafiya da tsaro na cikin hadari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris

A Gaza fiye da mutane 1,000 ne Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga watan Maris, tun bayan sake dawo da yaki a Zirin.

Hakan ya sanya adadin falasdinawan da Isra’ila ta kashe tun watan Oktoba ya kai 50,350 tare da raunata 114,400 a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.

Hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza sun kashe akalla Falasdinawa 80 a ranar Lahadi.

Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta ce, an kai mutane 53 da lamarin ya rutsa da su zuwa asibitoci a Gaza a ranar Lahadin, wato ranar farko ta bikin Eid al-Fitr.  

Ma’aikatar ta kara da cewa, “har yanzu da yawan wadanda abin ya shafa na makale a karkashin baraguzan gine-gine, saboda masu ceto ba su iya kai musu dauki.

A ranar 18 ga Maris, ne Isra’ila ta sake dawo da kai farmaki Gaza wanda ya saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni da ta fara aiki a watan Janairu.

Ana kuma tuhumar Isra’ila da laifin kisan kiyashi a gaban kotun kasa da kasa saboda yakin da ta yi da yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  •  Kasashen Iran Da Tunisya Suna Shirin Bunkasa Alaka A Fagagen Yawon Bude Ido
  • Hamas A Gaza Ta Amince Da Kafa Gwamnatin Hadin Kan Falasdinawa, Amma Makamanta Jan Layi Ne
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Karrama Hakimai Da Limamai Da Kayan Sallah
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Fiji: Ya Kamata A Koyi Fasahohin Da Kasar Sin Ta Samu A Fannin Raya Kasa
  • Karamar Hukumar Jahun Ta Bada Tallafin Noman Rani Ga Manoma 300
  • Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya
  • Wani Jami’in Leken Asirin HKI Ya Bukaci Kasashen Afirka Su Taimaka Su Karmi Falasdinawan Da Za;a Kora Daga Gaza