Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-22@04:35:54 GMT

An Kaddamarda Shirin Wayarda Kai Kan Hajjin Bana A Kaduna 

Published: 29th, January 2025 GMT

An Kaddamarda Shirin Wayarda Kai Kan Hajjin Bana A Kaduna 

 

Hukumar kulada jin daɗin alhazai ta jihar Kaduna ta shirya fara shirin wayar da kai da ilmantarwa ga maniyyata aikin hajjin bana.

 

Shugaban hukumar, Malam Salihu Abubakar, zai kaddamar da shirin ne a Cibiyar Wayar da Kai ta Alhazai da ke Dogarawa, shekkwatar karamar hukumar Sabon Gari.

 

“Shirin horon wayar da kai yana nufin ilmantar da maniyyata kan dukkan muhimman abubuwan da suka shafi aikin hajji,” in ji shi.

 

Wadannan sun haɗa da ilimin sanin ka’idojin shari’ar Musulunci da dokokin aikin hajji, da kuma warware matsalolin da ka iya tasowa domin tabbatar da sauƙi da ingantaccen hajji ga dukkan maniyyata.

 

Ya kuma bayyana cewa dukkan maniyyata, da waɗanda ke son yin rijista kafin ranar karshe ta biyan kuɗin aikin hajji, wato Juma’a, 31 ga Janairu, 2025, su halarta domin samun cikakken bayani.

 

Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kaddamarda

এছাড়াও পড়ুন:

Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome

Yau Asabar Washington da Tehran, ke tattauanwa a birnin Rome na kasar Italiya, wace ita ce ta biyu a shiga tsakanin kasar Oman kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Tattaunwar wacce ba ta gaba-da-gaba ba an gudanar da irin ta a ranar Asabar data gabata a birnin Muscat na kasar Oman, inda bangarorin biyu suka bayyana tattaunawar da mai armashi.

Gabanin tattaunawar ta yau, Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce akwai yuwuwar kulla yarjejeniya da Amurka idan har Washington ba ta gabatar da wasu bukatu na da suka wuce da tunani ba”.

Araghchi ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov, a ranar Juma’a a birnin Moscow, gabanin tattaunawar ta biyu tsakanin Tehran da Washington, da ake shirin gudanarwa yau a birnin Rome na kasar Italiya.

“Za mu tattauna kan batun nukiliya ne kawai, kuma ba za a saka wasu batutuwa a cikin wannan tattaunawar ba,” in ji shi.

Ya kara da cewa “Ina ganin mai yiyuwa ne a cimma matsaya idan [Amurkawa] suka nuna da gaske su ke kuma ba su gabatar da bukatu da ba su dace ba.

Sai dai ya jaddada cewa: “Hanyar diflomasiya a bude take, amma ya nuna matukar shakku game da aniyar Amurka idan aka yi la’akari da matsayin Washington da ke cin karo da juna.

“Muna da matukar shakku game da aniya da manufar bangaren Amurka, amma za mu shiga shawarwarin tare da azama.”Ya kuma jaddada aniyar Tehran ta ci gaba da samar da hanyoyin warware shirinta na nukiliya cikin lumana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika
  • Ministan HarkokinWajen Iran Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Swaitzerland Da Pakistan Ta Wayar Tarho
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Bada Tallafin Kudi Ga Manoman Alkama
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • An Rantsar Da Shugabanin Kungiyar KekeNapep A Kaduna
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila
  • Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
  • Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?
  • Iran Da Amurka Za Su Ci Gaba Da Tattaunawa Kan Shirin Nukiliyar Tehran
  • Iran da Amurka na shirin tattaunawa ta biyu a birnin Rome