Majalisar Dokokin Amurka zata dauki matakin fitar da dokar da zata hukunta kotun hukunta manyan laifuka ta duniya saboda kotun ta tabbatar da zarge-zargen manyan laifukan gwamnatin mamayar Isra’ila

Ana sa ran nan kusa kadan Majalisar Dattawan Amurka za ta fara kada kuri’a kan kakaba takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta duniya da ke birnin Hague, bayan da kotun ta tuhumi fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohun ministan yakinsa Yoav Gallant a watan Mayu da aikata laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Zirin Gaza.

A cewar jaridar Washington Post, ‘yan majalisar dokokin Amurka suna matsawa wajen zartar da dokar, wadda za ta sanya takunkumi kan kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa, yayin da wasu daga cikin manyan kawayen Amurka na kasashen Turai suke fargabar cewa: Dokar za ta gurgunta babbar kotun hukunta manyan laifukan ta duniya tare da baiwa masu aikata laifukan yaki damar cin karensu ba babbaka ba tare hukunta su ba, kuma hakan zai raunana mutuncin kasashen yamma”.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kotun hukunta manyan

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji

Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta yi watsi da rahoton da sojin Isra’ila suka fitar kan kisan da aka yi wa sama da jami’an agajin gaggawa na Gaza a watan da ya gabata, wanda gwamnatin kasar ta ce an kashe ne ta bisa kuskure.

Kungiyar ta yi fatali da rahoton na Isra’ila da cewa ba shi da inganci kuma ba za a amince da shi ba, tana mai jaddada cewa yana cike da karairayi.

A wani rahoto da suka fitar ka abinda ya faru sojojin Isra’ila sun yi ikirarin cewa, an samu ” kura-kurai da yawa” a kisan da akayi wa jami’an agajin a Gaza, suna masu cewa za a kori wani kwamandan sojoji.

“Binciken ya nuna cewa an samu wasu matsaloli na rashin da’a na kwararru, da rashin bin umarni, da kuma gaza yin cikakken bayani kan lamarin,” in ji rundunar.

A ranar 23 ga Maris, ne aka harbe wasu ma’aikatan agaji na Falasdinawa 15 da masu aikin ceto a kusa da Rafah da ke kudancin Gaza.

Sojojin Isra’ila sun sake nanata cewa shida daga cikin likitocin Falasdinawa 15 da Isra’ila ta kashe, ‘yan kungiyar Hamas ne.

Kisan da akayi wa jami’an agajin gaggawa na falasdinu ya fuskanci tofin Allah-tsine daga kasashen duniya da kungiyoyin kasa da kasa da dama.

Lamarin dai ya sake fiddo a fili irin ta’asar da Isra’ila ke aikatawa a zirin Gaza.

Da farko dai Isra’ila ta yi ikirarin cewa sun bude wuta ne, saboda yadda motocin suka nufo, a cikin dare, ba fitilu, kuma babu wata masaniya da sojinta suke da a kan zuwan motocin.

Amma kuma daga baya hukumar sojin ta ce, wannan bayani da ta bayar akwai kuskure, bayan da aka gano wani hoton bidiyo a wayar daya daga cikin ma’aikatan agajin da sojin Isra’ilar suka kashe a wannan hari, hoton da ke nuna motocin na tafiya da fitilu a kunne da kuma duk wata alama da za ta fayyace su waye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ba Ta Da Niyyar Tattaunawa Da Amurka A Fili Bainar Jama’a Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta Amnesty International Ta Ce; Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ba Ta Dace Da Bincike Laifukan Sojojinta Ba
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Gharibabadi : inganta sinadarin uranium jan layi ne a tattaunawar Iran da Amurka
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Iran Ta Yi Watsi Da Barazanar HKI
  • Demokradiyyar Kwango Ta Haramta Jam’iyyar Josept Kabila A Kasar Saboda Hulda Da Yan Tawaye
  • Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila