Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Dole ne kasashen duniya su gane irin wahalhalun da al’ummar Iran ta sha wajen yaki da ta’addanci

Jakadan kasar Iran na dindindin a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’id Irawani ya aike da wasika ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya dangane da laifukan da kungiyar ta’addanci ta munafukai {MKO} ta aikata, wanda ya yi sanadin shahadan mutane 23,323, Irawani ya bukaci kungiyoyin kasa da kasa sun yi furuci da ire-iren wahalhalun da al’ummar Iran suka sha tsawon shekaru da dama da kuma wadanda suka yi shahada a fagen yaki da ta’addanci.

A cikin wannan sakon, Irawani ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta himmatu wajen aiwatar da dokokin kasa da kasa da suka shafi yaki da ta’addanci da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, kuma wajibi ne al’ummar duniya su gane irin wahalhalun da al’ummar Iran suka sha tsawon shekaru da dama a sakamakon yaki da suke yi da ta’addanci.

Ya yi nuni da cewa “ya zama dole a saurari tare da mutunta bukatun iyalan wadanda abin ya shafa, ba tare da nuna siyasar fuska biyu ko kuma yin zarge-zarge marasa tushe ba.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yaki da ta addanci

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha

Yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da Sergei Shoigu, sakataren majalisar tsaro ta kasar Rasha, a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Xi Jinping ya ce, Sin da Rasha sun kasance masu tuntubar juna a dukkan matakai, da aiwatar da matsayar da suka cimma da shugaba Putin da hadin gwiwa mai muhimmanci da moriyar juna tare da zurfafa hadin gwiwarsu a kai a kai, domin taimakawa muradunsu na bai daya na samun ci gaba da farfado da kasashen biyu. Ya kara da cewa, ya kamata kasashen 2 su karfafa hadin kai a harkokin da suka shafi yanki da ma duniya, su kuma goyi bayan rawar da kasashen BRICS da kungiyar hadin kai ta Shanghai suke takawa, tare da karfafa saita alkiblar hadin gwiwa da goyon bayan juna tsakanin kasashe masu tasowa.

A nasa bangare, Sergei Shoigu ya ce, Sin da Rasha sun kai wani matsayi da ba a taba gani ba, kuma ba su yi hakan don muzgunawa wata kasa ba. Ya ce, haduwar Sin da Rasha ta taka muhimmiyar rawa a duniya, kuma ta nuna misalin dangantaka tsakanin manyan kasashe. Ya ce, Sin da Rasha za su ci gaba da kasancewa masu aminci da juna da tattaunawa bisa daidaito, kuma muhimmin hadin gwiwar dake tsakaninsu, ya dace da muradunsu na bai daya. Bugu da kari, ya ce, Rasha za ta aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen 2 suka cimma tare da karfafa dangantakarta da Sin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka ta Kudu da Malaysia da Colombiya za su hana jiragen ruwa da ke dauke da makamai zuwa Isra’ila
  • Yemen Ta Ce A Shirye Take Ta Koma Yaki Idan Yaki Ya Sake Barkewa A Gaza
  • Noman Rani: Tinubu Ya Amince Da Fadada Madatsun Ruwa 12 A Nijeriya
  • Shugaban Sin Ya Gana Da Sakataren Majalisar Tsaron Rasha
  • Majalisa Za Ta Binciki INEC Kan Jinkirin Gudanar Da Zaben Cike Gurbi
  • A gaban mijina Akpabio ya fara neman kwanciya da ni —Sanata Natasha
  • Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • NAFDAC Ta Kaddamar Da Sabbin Shirye-Shiryen Yaki Da Jaribun Magunguna
  • Iran Da Saudiyya Sun Tattauna Kan Taron OIC Mai Zuwa