Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Duk wani hari da aka kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran zai fuskanci mayar da martani cikin gaggawa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Harin da Amurka da yahudawan sahayoniyya suke kai wa kan cibiyoyin nukiliyan kasashe, nau’in hauka ne kuma zai jefa yankin cikin bala’i.

A cikin wata sanarwa da ya aikewa gidan talabijin na Sky News a ranar Talata, Araqchi ya sake jaddada matsayin Iran na cewa: “Duk wani hari da za a kai wa cibiyoyin nukiliyar kasarsa zai fuskanci mayar da martani cikin gaggawa da azama,” ya kara da cewa: “Ba ya jin za a aiwatar da irin wannan aikin wauta kan Iran, hasali ma, hakan wani nau’in hauka ne kuma zai wurga yankin cikin mummunan bala’i.”

Dangane da yiwuwar tattaunawa da Amurka da kalaman shugaban Amurka Donald Trump game da warware takaddamar ta hanyar diflomasiyya, Araqchi ya jaddada cewa: “Sabuwar yarjejeniyar da za a kulla da Iran zata kasance mai kyau.” Ya kara da cewa: yanayi ya canja da matakan baya saboda akwai ayyuka masu yawa wanda dole ne ga ɗaya bangaren ya ɗauki matakin dawo da kwarin gwiwa, duk da har yanzu Iran ba ta ji komai daga gare shi ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi

A safiyar yau litinin ce a nan Iran da kuma wasu kasashen duniya da dama suka gudanar da sallar Idi wanda ya kawo karshen watan Ramadan mai al-farma wanda musulmi suka yi azuminsa daga safe zuwa faduwar rana na tsawon kwanaki 29-ko 30.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa a nan Tehran dubban daruruwan mutanen suka fito zuwa babbar masallacin Imam Khumaini dake tsakiyar birnin Tehran inda suka gudanar da sallah mai raka’o’I biyu tare da jagorancin Jagoran juyin juya halin musulunci a kasar Imam Sayyid Aliyul Khamina’e.

Duk da cewa ana samun babbanci tsakanin musulmi kan ranar ajiye azumun amma akalla ba wanda zai yi azami kasa da kwanaki 29.

A cikin watan dai, musulmi sukan yawaita karatun alkur\ani mai girma da kuma kokarin sanin ma’anarsa da kuma zrfafa tunani a cikinsa.

Har’ila yau watan ne na yawaita sadaka na abinci da kuma duk abinda zai taimakawa masu karamin karfi a tattalin arziki.

Musulmi sukan yawaita addu’a da neman gafarar All..a kan zunubban da suka aiakata sannan suna yawaita salloli.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DG VON Yayi Kira Ga Zaman Lafiya Da Hadin Kai Don Fadada Ci gaban Tattalin Arziki Da Ci Gaba.
  • Kungiyar “Amnesty” Na Zargi Netanyahu Da Aikata Laifukan Yaki
  •  Larijani:  Dole Iran Ta Kera Makaman Nukiliya Idan Amurka Da Isra’ila Su Ka Kawo Ma Ta Hari
  • Iran ta mayar wa Amurka martani kan barazanar kai mata hari
  • Iran ta gargadi Amurka kan barazanar harin bam da Trump ya yi
  • A Yau Litinin Ce Aka Gudanar Da Sallar Edi Da Bukukuwan Sallah A Nan Iran Da Wasu Kasashen Musulmi
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Pezeshkian: Iran Ba Za Ta Yi Tattaunawa Kai Tsaye Da Amurka Ba
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya