Aminiya:
2025-04-23@06:41:31 GMT

Jirgin Max Air ɗauke da fasinjoji 59 ya tsallake rijiya da baya a Kano

Published: 29th, January 2025 GMT

Wani jirgin kamfanin Max Air ya tsallake rijiya da baya yayin sauka a filin jirgin Malam Aminu Kano (MAKIA) a ranar Talata da daddare.

Jirgin wanda yake ɗauke da fasinjoji 53 da ma’aikata shida yana dawowa daga Jihar Legas ne lokacin da haɗarin ya faru.

Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS? Mun kama mutum 46 da miyagun ƙwayoyi a Yobe — NDLEA

Wani fasinja ya bayyana cewa jirgin ya rasa tayar gabansa yayin sauka a filin jirgin.

Fasinjan ya yi karin bayani da cewa cewa tayar jigin ta fashe sannan ta kama da wuta a daidai lokacin da ya sauka cikin filin da misalin karfe 10:19 na dare.

“Daidai lokacin da tayar ta taɓa ƙasa sai ta kama da wuta, hayaki ya turnuke a cikin jirgin wanda ya sa dole muka fita ta ƙofar fitar gaggawa.

“Yayin da muke fitowa daga jirgin, wasu ’yan kashe gobara sun riga sun fara watsa wa jirgin ruwa domin kashe wutar.”

Da yake zantawa da manema labarai, Manajan Max Air reshen Jihar Kano, Malam Bello Ramalan, ya ce ba a samu asarar rai ko jin rauni ba.

“Ina ba da haƙuri bisa matsalar da ta faru, kuma muna godiya ga Allah bisa tseratar da fasinjojin da Ya yi. Ni lafiyar fasinjoji ce a gabana.

“Dangane da bin dokokin saukar jiki, kamfaninmu ya bi ka’idojin da suka dace na yin saukar gaggawa, wanda Allah Ya sa abin ya zo da sauƙi.

“Ka’idojin sun hada da fitar da fasinjoji cikin gaggawa, killace matuƙa jirgin da kuma haɗa kai da hukumomin bincike.”

Kamfanin Max Air ya ce yana aiki tare da hukumar binciken haɗuran jiragen sama AIB da AED domin bincike kan dalilin aukuwar lamarin.

Malam Ramalan ya ce “bincike na farko ya nuna cewa matsalar tayar jirgin ce ta haddasa haɗarin.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya

An samu rahoton cewa, Fursunoni tara a gidan yari na Oko Erin a jihar Kwara a ranar 19 ga watan Afrilu, sun tsere. Majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zagazola Makama cewa, da misalin karfe 10:00 na dare, wani ma’aikaci a gidan, mai suna Joseph Issa, ya sanar da faruwar lamarin. Rugujewar Gini A Legas: Adadin wadanda Suka Mutu Ya Kai Biyar, An Ceto 20 Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia Ba tare da bata lokaci ba, ‘yansanda suka yi gaggawar isa wurin, inda suka sake kama daya daga cikin wadanda suka tsere, mai suna Abdul Raman Misa mai shekaru 15. An mayar da Misa gidan yarin, yayin da ake ci gaba da neman sauran takwas din da suka arce. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da bincike kan yadda suka tsere.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno 
  • Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
  • Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta Amnesty International Ta Ce; Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ba Ta Dace Da Bincike Laifukan Sojojinta Ba
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • Fursunoni 9 Sun Tsere Daga Gidan Gyara Hali A Jihar Kwara, An Cafko Guda Daya