Aminiya:
2025-04-02@01:32:53 GMT

Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Published: 29th, January 2025 GMT

Jami’an tsaro sun mamaye Sakatariyar Jam’iyyar PDP, bayan rikici ya ɓarke kan shugabancin jam’iyyar.

Rikicin ya kunno kai ne tsakanin Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye kan wanda ke da haƙƙin zama Sakataren jam’iyyar na ƙasa.

Matashiyar da ta watsa wa mai naƙuda tafasasshen ruwa ta shiga hannu Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?

Rikicin ya fara ne lokacin da duka mutane biyun suka iso taron kwamitin amintattun.

A lokacin taron, wani hadimin Anyanwu ya tilasta wa Ude-Okoye fita daga zauren taron, wanda hakan ya janyo gardama tsakanin magoya bayan ɓangarorin biyu.

Jami’an tsaro sun shiga tsakani domin kwantar da tarzoma.

Matsalar ta samo asali ne bayan Anyanwu ya yi murabus daga kujerarsa don tsayawa takarar Gwamnan Jihar Imo, takarar da bai yi nasara ba.

A lokacin da ba ya nan, ɓangaren jam’iyyar na Kudu maso Gabas ya naɗa Ude-Okoye a matsayin sabon sakataren jam’iyyar.

Amma bayan Anyanwu ya faɗi a zaɓen gwamna, ya yi ƙoƙarin karɓe kujerarsa a jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa rikici.

A ranar 20 ga watan Disamban 2024, kotun ɗaukaka ƙara da ke Enugu ta tabbatar da hukuncin wata babbar kotu da ta tuɓe Anyanwu daga kujerar sakataren jam’iyyar, tare da tabbatar da Ude-Okoye a matsayin halastaccen sakatare.

Anyanwu ya ɗaukaka ƙara tare da neman dakatar da hukuncin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakatare Sakatariya

এছাড়াও পড়ুন:

Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya

Miliyoyin Musulmi ne a faɗin duniya ke bikin Ƙaramar Sallah bayan kammala azumin Ramadana.

Ku ci gaba da kasancewa da shafin Aminiya domin samun hotunan yadda aka gudanar da Sallar Idi a wasu sassan duniya da kuma nan gida Nijeriya.

Musulmi a Filin Idi na Kubwa da ke birnin Abuja Wasu da suka fito sallar idi bayan wani coci da ke daura da Filin Idin Kubwa da ke Abuja Masallata a Filin Idi da ke garin Kafanchan Filin Idin garin Kafanchan

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe yara 322 cikin kwanaki 10 a Gaza — UNICEF
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Ƴansanda Sun Kama Wanda Ya Kashe Ɗan Bijilanti A Tawagar Sarki Sunusi II
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • Hotunan Sallar Idi daga sassan duniya
  • Bayan Hukuncin ‘Yansanda, Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah
  • ‘Yan Hamayyar Siyasar A Kasar Turkiya Suna Ci Gaba Da Yin Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • An Gudanar Da Gagarumar Zanga- Zanga Ta Ranar Qudus Ta Duniya A Birnin Roma Na Kasar Italiya