Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka
Published: 29th, January 2025 GMT
Sama da ’yan Najeriya 5,000 da ke zaune a Amurka ba bisa ƙa’ida ba, na fuskantar barazanar dawo da su gida.
Daga cikinsu, kusan 1,500 ne ake tsare da su, wanda hakan na daga cikin matakin da sabon Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ɗauka na korar baƙin haure da masu neman mafaka ba bisa ƙa’ida ba.
Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?Alƙaluman da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Amurka (ICE), ta fitar a watan Nuwamban 2024, sun nuna cewa akwai mutum miliyan 1.
Sai dai sabbin alƙaluman da ICE ta sake fitarwa, sun nuna cewa an ƙara samun wasu mutum 1,454 daga Najeriya da ake tsare da su, kuma ana shirin dawo da su gida.
Hukumar ta ce daga cikin waɗanda ake tsare da su, 772 na jiran hukunci, yayin da aka riga an yanke wa wasu hukunci saboda laifuka daban-daban, ciki har da na karya dokokin shige da fice.
Duk da cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.
Sai dai hukumar da ke kula da ’yan Najeriya a ƙasashen waje ta ce ta kafa wani kwamiti da zai binciki matsalar tare da duba hanyoyin da za a bi domin magance ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun yi basaja da kayan EFCC wajen sace mutum 10 a otal
Wasu ’yan bindiga sun yi basaja a matsayin jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), tare da sace mutum 10 a Otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Ƙaramar Hukumar Chanchaga a Jihar Neja.
Wani masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 4:58 na asubar ranar Talata, 27 ga watan Fabrairu, 2025.
Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a Kano Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a BauchiRahotanni sun bayyana cewa maharan sun isa otal ɗin ne, inda suka yi basaja a matsayin jami’an EFCC da ke bakin aiki.
Sun fara da kashe na’urorin CCTV na otal ɗin kafin su kutsa cikin ɗakunan baƙi, inda suka kwashe mutum 10 suka tafi da su ba tare da sanin inda suka nufa ba.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ya ce suna gudanar da bincike don gano waɗanda suka aikata laifin da kuma ceto waɗanda aka sace.
Hukumomi sun buƙaci jama’a da su kasance masu sanya ido tare da sanar da hukumomin tsaro idan sun ga wani abin da ke da ɗaukar hankali.