Aminiya:
2025-04-02@06:21:46 GMT

Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka

Published: 29th, January 2025 GMT

Sama da ’yan Najeriya 5,000 da ke zaune a Amurka ba bisa ƙa’ida ba, na fuskantar barazanar dawo da su gida.

Daga cikinsu, kusan 1,500 ne ake tsare da su, wanda hakan na daga cikin matakin da sabon Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ɗauka na korar baƙin haure da masu neman mafaka ba bisa ƙa’ida ba.

Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici Me kuka sani game da ficewar Mali, Nijar, da Burkina Faso daga ECOWAS?

Alƙaluman da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Amurka (ICE), ta fitar a watan Nuwamban 2024, sun nuna cewa akwai mutum miliyan 1.

445 baƙin haure da ke zaune a ƙasar ba tare da takardun izini ba, ciki har da mutum 3,690 daga Najeriya.

Sai dai sabbin alƙaluman da ICE ta sake fitarwa, sun nuna cewa an ƙara samun wasu mutum 1,454 daga Najeriya da ake tsare da su, kuma ana shirin dawo da su gida.

Hukumar ta ce daga cikin waɗanda ake tsare da su, 772 na jiran hukunci, yayin da aka riga an yanke wa wasu hukunci saboda laifuka daban-daban, ciki har da na karya dokokin shige da fice.

Duk da cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

Sai dai hukumar da ke kula da ’yan Najeriya a ƙasashen waje ta ce ta kafa wani kwamiti da zai binciki matsalar tare da duba hanyoyin da za a bi domin magance ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar

Tawagogin ma’aikatan ceto na kasar Sin na ci gaba da aiki a yankin da ya fi shan wuya na Mandalay da ke tsakiyar kasar Myanmar, sakamakon girgizar kasar da ta afku mai karfin maki 7.9 a makon da ya gabata, inda zuwa yanzu suka ceci mutum takwas da suka tsira daga ibtila’in, da misalin karfe 8 na safiyar ranar Talata, agogon kasar.

A yayin bikin bayar da gudummawar kudi ga wadanda girgizar kasar ta shafa a birnin Nay Pyi Taw a yau Talata, shugaban majalisar gudanarwar kasar Myanmar, Min Aung Hlaing, ya ce, mutanen da suka mutu sakamakon mummunar girgizar kasar wacce ta afku a kasar a ranar Jumma’a, sun kai 2,719, yayin da wasu 4,521 suka jikkata, kana 441 suka bace ba a ji duriyarsu ba har yanzu, kamar yadda kafafen yada labarai na kasar suka ruwaito. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Arewa Ke Tafiya Kudu Farauta
  • Ma’aikatan Kasar Sin Sun Ceto Mutum 8 Zuwa Yanzu A Myanmar
  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Za Su Kwaɗaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
  • Kasar Sin Ta Nanata Adawa Da Matakan Tilastawa Da Nuna Babakeren Tattalin Arziki
  • Muna so a nuna wa duniya mutanen da suka kashe ’yan Arewa a Edo — Gwamnan Kano
  • Jagora : A yau, duniyar musulmi tana bukatar hadin kai
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya